< Isaiah 40 >

1 “Be consoled, be consoled, O my people!” says your God.
Ta’aziyya, ku ta’azantu mutanena, in ji Allahnku.
2 Speak to the heart of Jerusalem, and call out to her! For her malice has reached its end. Her iniquity has been forgiven. She has received double for all her sins from the hand of the Lord.
Yi magana mai kwantar da rai ga Urushalima, ku kuma furta mata cewa aiki mai zafinta ya isa, cewa an fanshi zunubinta, cewa ta karɓi daga hannun Ubangiji ninki biyu saboda dukan zunubanta.
3 The voice of one crying out in the desert: “Prepare the way of the Lord! Make straight the paths of our God, in a solitary place.
Muryar wani tana kira cewa, “A cikin hamada ku shirya hanya saboda Ubangiji; ku miƙe manyan hanyoyi domin Allahnmu a cikin jeji.
4 Every valley will be exalted, and every mountain and hill will be brought low. And the crooked will be straightened, and the uneven will become level ways.
Za a cike kowane kwari, a baje kowane dutse da kowane tudu; za a mayar da karkatattun wurare su zama sumul, munanan wurare kuma su zama da kyau.
5 And the glory of the Lord will be revealed. And all flesh together will see that the mouth of the Lord has spoken.”
Za a kuma bayyana ɗaukakar Ubangiji, dukan mutane kuwa za su gan ta. Gama Ubangiji da kansa ne ya yi magana.”
6 The voice of one saying, “Cry out!” And I said, “What should I cry out?” “All flesh is grass, and all its glory is like the flower of the field.
Muryar tana cewa, “Ka yi shela.” Na kuwa ce, “Me zan yi shelar?” “Dukan mutane kamar ciyawa suke, kuma dukan ɗaukakarsu kamar furannin jeji ne.
7 The grass has dried up, and the flower has fallen. For the Spirit of the Lord has blown over it. Truly, the people are like grass.
Ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, domin Ubangiji ya hura iska a kansu. Tabbatacce mutane ciyawa ne.
8 The grass has dried up, and the flower has fallen. But the Word of our Lord remains for eternity.”
Hakika ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, amma maganar Allahnmu tana nan daram har abada.”
9 You who evangelize Zion, climb a high mountain! You who evangelize Jerusalem, lift up your voice with strength! Lift it up! Do not be afraid! Say to the cities of Judah: “Behold, your God!”
Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Sihiyona, ka haura a bisa dutse. Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Urushalima, ka tā da muryarka ka yi ihu, ka ɗaga ta, kada ka ji tsoro; faɗa wa garuruwan Yahuda, “Ga Allahnku!”
10 Behold, the Lord God will arrive in strength, and his arm will rule. Behold, his reward is with him, and his work is before him.
Duba, Ubangiji Mai Iko Duka yana zuwa da iko, hannunsa kuma yana yin mulki dominsa. Duba, ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa kuma na rakiyarsa.
11 He will pasture his flock like a shepherd. He will gather together the lambs with his arm, and he will lift them up to his bosom, and he himself will carry the very young.
Yakan lura da garkensa kamar makiyayi. Yakan tattara tumaki wuri ɗaya yă riƙe su kurkusa da ƙirjinsa; a hankali kuma yakan bi da masu ba da mama.
12 Who has measured the waters in the hollow of his hand, and who has weighed the heavens with his palm? Who has suspended the mass of the earth with three fingers, and who has weighed the mountains on a balance and the hills on a scale?
Wane ne ya auna ruwaye a tafin hannunsa, ko kuwa ya gwada tsawon sammai da fāɗin tafin hannunsa? Wane ne ya riƙe ƙurar ƙasa a kwando, ko kuwa ya auna nauyin duwatsu a magwaji, tuddai kuma a ma’auni?
13 Who has assisted the Spirit of the Lord? Or who has been his counselor and has revealed things to him?
Wane ne ya fahimci zuciyarUbangiji, ko kuwa ya koya masa a matsayin mashawarcinsa?
14 With whom has he consulted? And who has instructed him, and taught him the path of justice, and guided him to knowledge, and revealed the way of understanding to him?
Wane ne Ubangiji ya nemi shawararsa don yă ganar da shi, wane ne kuma ya koya masa hanyar da ta dace? Wane ne ya koya masa sani ko ya nuna masa hanyar fahimta?
15 Behold, the nations are like a drop of water in a bucket, and they are considered as the smallest grain on a balance. Behold, the islands are like a little dust.
Tabbatacce al’ummai suna kama da ɗigon ruwa a cikin bokiti an ɗauke su a matsayin ƙura a kan magwaji; yakan auna tsibirai sai ka ce ƙura mai laushi.
16 And Lebanon will not be sufficient to start a fire, and its animals will not be sufficient for a burnt offering.
Itatuwan Lebanon ba su isa a yi wutar bagade da su ba, balle dabbobinsa su isa yin hadayun ƙonawa.
17 All the nations in his sight are as if they did not exist, and they are considered by him as if they were nothingness and emptiness.
A gabansa dukan al’ummai ba kome ba ne; ya ɗauke su ba a bakin kome ba kuma banza ne kurum.
18 Therefore, to whom would you liken God? Or with what image would you replace him?
To, ga wane ne za ka kwatanta Allah? Wace siffa za ka kwatanta shi da ita?
19 Should the workman cast a statue? Or has the goldsmith formed it with gold, or the silversmith with plates of silver?
Gunki dai, maƙeri kan yi zubinsa, maƙerin zinariya kuma yă ƙera shi da zinariya yă kuma sarrafa masa sarƙoƙin azurfa.
20 He has chosen strong wood that will not decay. The skillful artisan seeks a way to set up an idol that cannot be moved.
Mutumin da talauci ya sha kansa da ba zai iya miƙa irin hadayar nan ba kan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yakan nemi gwanin sassaƙa don yă sassaƙa masa gunkin da ba zai fāɗi ba.
21 Do you not know? Have you not heard? Has it not been announced to you from the beginning? Have you not understood the foundations of the earth?
Ba ku sani ba? Ba ku taɓa ji ba? Ba a faɗa muku daga farko ba? Ba ku fahimta ba tun kafawar duniya?
22 He is the One who sits upon the globe of the earth, and its inhabitants are like locusts. He extends the heavens as if they were nothing, and he spreads them out like a tent, in which to dwell.
Yana zaune a kursiyi a bisa iyakar duniya, kuma mutanenta suna kama da fāra. Ya miƙa sammai kamar rumfa, ya kuma shimfiɗa su kamar tentin da za a zauna a ciki.
23 He has brought those who examine what is secret to nothingness. He has brought the judges of the earth to emptiness.
Yakan mai da sarakuna ba kome ba yă mai da masu mulkin wannan duniya wofi.
24 And certainly, their stalk was neither planted, nor sown, nor rooted in the ground. He has suddenly blown across them, and they have withered, and a whirlwind will carry them away like chaff.
Ba da jimawa ba bayan an shuka su, ba da jimawa ba bayan an dasa su, ba da jimawa ba bayan sun yi saiwa a ƙasa, sai yă hura musu iska su yanƙwane, guguwa kuma ta kwashe su kamar yayi.
25 “And to whom would you compare me or equate me?” says the Holy One.
“Ga wa za ku kwatanta ni? Ko kuwa wa yake daidai da ni?” In ji Mai Tsarkin nan.
26 Lift up your eyes on high, and see who has created these things. He leads forth their army by number, and he calls them all by name. Because of the fullness of his strength and robustness and virtue, not one of them was left behind.
Ku ɗaga idanunku ku duba sammai. Wane ne ya halicce dukan waɗannan? Wane ne ya fitar da rundunar taurari ɗaya-ɗaya, yana kiransu, kowanne da sunansa. Saboda ikonsa mai girma da kuma ƙarfinsa mai girma, babu ko ɗayansu da ya ɓace.
27 Why do you say this, O Jacob, and why do you speak this way, O Israel? “My way has been hidden from the Lord, and my judgment escaped notice by my God.”
Ya Yaƙub, ya Isra’ila, me ya sa kake ce kana kuma gunaguni cewa, “Hanyata tana a ɓoye daga Ubangiji; Allah bai kula da abin da yake damuna ba”?
28 Do you not know, or have you not heard? The Lord is the eternal God, who has created the limits of the earth. He does not diminish, and he does not struggle. Neither is his wisdom searchable.
Ba ku sani ba? Ba ku ji ba? Ubangiji madawwamin Allah ne, Mahaliccin iyakokin duniya. Ba zai taɓa gaji ko yă kasala ba, kuma fahimtarsa ya wuce gaban ganewar mutum.
29 It is he who gives strength to the weary, and it is he who increases fortitude and strength in those who are failing.
Yakan ba da ƙarfi ga waɗanda suka gaji yă kuma ƙara ƙarfi ga marasa ƙarfi.
30 Servants will struggle and fail, and young men will fall into infirmity.
Ko matasa ma kan gaji su kuma kasala, samari kuma kan yi tuntuɓe su fāɗi;
31 But those who hope in the Lord will renew their strength. They will take up wings like eagles. They will run and not struggle. They will walk and not tire.
amma waɗanda suka dogara ga Ubangiji za su sabunta ƙarfinsu. Za su yi firiya da fikafikai kamar gaggafa; za su kuma yi gudu ba kuwa za su gaji ba, za su yi tafiya ba kuwa za su kasala ba.

< Isaiah 40 >