< Isaiah 4 >

1 And seven women will take hold of one man, in that day, saying, “We will eat our own bread and wear our own clothing, only let us be called by your name, so as to take away our reproach.”
A wannan rana mata guda bakwai za su cafke namiji guda su ce, “Ma ciyar da kanmu mu kuma yi wa kanmu sutura; ka dai bari mu ce kai ne mijinmu. Ka ɗauke mana kunyar da za mu sha.”
2 In that day, the seedling of the Lord will have magnificence and glory, and the fruit of the earth will be greatly-esteemed and a source of joy to those who will have been saved out of Israel.
A wannan rana Reshen Ubangiji zai zama kyakkyawa da kuma ɗaukaka, kuma amfanin ƙasar zai zama abin fariya da ɗaukakar waɗanda suka rayu a Isra’ila.
3 And this shall be: all who are left behind in Zion, and who remain in Jerusalem, shall be called holy, all who have been written in life in Jerusalem.
Waɗanda suka rage a Sihiyona, waɗanda suka rage a Urushalima, za a ce da su masu tsarki, wato, dukan waɗanda aka rubuta a cikin masu rai a Urushalima.
4 Then the Lord will have washed away the filth of the daughters of Zion, and will have washed away the blood of Jerusalem from its midst, by means of a spirit of judgment and a spirit of intense devotion.
Ubangiji zai wanke duk wani ƙazantar matan Sihiyona; ya tsabtacce jinin da aka zubar daga Urushalima ta wurin ruhun hukunci da yake ƙuna kamar wuta.
5 And the Lord will create, over every place of Mount Zion and wherever he is called upon, a cloud by day and a smoke with the splendor of burning fire by night. For protection will be over every glory.
Sa’an nan Ubangiji zai sa girgijen hayaƙi da rana da harshen wuta da dare a bisa dukan Dutsen Sihiyona da kuma bisa waɗanda suka tattaru a can; a bisa duka kuwa ɗaukakar za tă zama rumfa.
6 And there will be a tabernacle for shade from the heat in daytime, and for security, and for protection from the whirlwind and from rain.
Za tă zama rumfa da inuwar da za tă tare zafin rana, da kuma mafaka da wurin ɓuya daga hadari da ruwan sama.

< Isaiah 4 >