< Isaiah 39 >

1 At that time, Merodach Baladan, the son of Baladan, the king of Babylon, sent letters and gifts to Hezekiah. For he had heard that he had fallen ill and had recovered.
A wannan lokaci Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu da kuma kyauta, domin ya ji rashin lafiyarsa da kuma warkarwarsa.
2 And Hezekiah rejoiced over them, and he showed them the storehouses of his aromatic spices, and of the silver and gold, and of the perfumes and precious ointments, and all the repositories for his belongings, and all the things that were found in his treasures. There was nothing in his house, nor in all his dominion, that Hezekiah did not show them.
Hezekiya ya marabci jakadun da murna ya kuma nuna musu abin da gidajen ajiyarsa sun ƙunsa, azurfa, zinariya, yaji, tatsatsen mai, dukan kayan yaƙinsa da kuma kome da yake a ma’ajinsa. Babu abin da yake a cikin fadansa ko cikin dukan masarautarsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
3 Then Isaiah the prophet entered before king Hezekiah, and he said to him, “What did these men say, and from where did they come to you?” And Hezekiah said, “They came to me from a far away land, from Babylon.”
Sai Ishaya annabi ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya kuma tambaye shi ya ce, “Mene ne waɗannan mutane suka faɗa, kuma daga ina suka fito?” Hezekiya ya amsa ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Sun zo ne daga Babilon.”
4 And he said, “What did they see in your house?” And Hezekiah said: “They have seen all the things that are in my house. There was nothing that I did not show them among my treasures.”
Annabi ya yi tambaya ya ce, “Mene ne suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Sun ga kome da kome a fadana. Babu abin da ban nuna musu a cikin ma’ajina ba.”
5 And Isaiah said to Hezekiah: “Hear the word of the Lord of hosts:
Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji maganar Ubangiji Maɗaukaki.
6 Behold, the days are coming when all that is in your house, and all that your fathers have stored up, even to this day, will be taken away to Babylon. There will be nothing left behind, says the Lord.
Tabbatacce lokaci yana zuwa sa’ad da kome da yake cikin fadanka, da kuma dukan abin da kakanninka suka ajiye har yă zuwa yau, za a kwashe zuwa Babilon babu abin da za a bari, in ji Ubangiji.
7 And your children, who will issue from you, whom you will produce, they will be taken away. And they will become eunuchs in the palace of the king of Babylon.”
Waɗansu cikin zuriyarka, nama da jininka waɗanda za a haifa maka, za a kwashe su a tafi, za su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
8 And Hezekiah said to Isaiah, “The word of the Lord which he has spoken is good.” And he said, “But let there be peace and truth in my days.”
Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka yi tana da kyau.” Gama ya yi tunani a ransa cewa, “Salama da kāriya za su kasance a zamanina.”

< Isaiah 39 >