< Isaiah 36 >

1 And it happened that, in the fourteenth year of king Hezekiah, Sennacherib, the king of the Assyrians, went up against all the fortified cities of Judah, and he seized them.
A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin Sarki Hezekiya, Sennakerib sarkin Assuriya ya kai wa dukan birane masu kagaran Yahuda yaƙi ya kuma kame su.
2 And the king of the Assyrians sent Rabshakeh from Lachish into Jerusalem, to king Hezekiah, with a great force, and he stood near the aqueduct of the upper pool, at the road to the fuller’s field.
Sai sarkin Assuriya ya aiki sarkin yaƙinsa tare da mayaƙa masu yawa daga Lakish zuwa wurin Sarki Hezekiya a Urushalima. Sa’ad da sarkin yaƙi ya tsaya a wuriyar Tafkin Tudu, a hanya zuwa Filin Mai Wanki,
3 And those who went to him were Eliakim, son of Hilkiah, who was over the house, and Shebna, the scribe, and Joah, son of Asaph, the historian.
Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka fita zuwa wurinsa.
4 And Rabshakeh said to them: “Tell Hezekiah: Thus says the great king, the king of the Assyrians: What is this faith in which you believe?
Sai sarkin yaƙin ya ce musu, “Ku faɗa wa Hezekiya. “‘Ga abin da babban sarki, sarkin Assuriya, ya faɗa. A kan me kake dangana wannan ƙarfin halinka?
5 And by what counsel or strength would you prepare to rebel? In whom do you have faith, so much so that you would withdraw from me?
Ka ce kana da dabara da kuma ƙarfin mayaƙa, amma kana magana banza ce kawai. Ga wa ka dogara, da kake tayar mini?
6 Behold, you are trusting in Egypt, in that broken staff of a reed. But if a man were to lean against it, it would enter his hand and pierce it. So is Pharaoh, the king of Egypt, to all who trust in him.
Yanzu duba, kana dogara ga Masar, wannan ɗan tsinken kyauron dogarawa, wanda zai soki hannun mutum yă kuma ji masa rauni in ya dangana a kansa! Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga duk wanda ya dogara da shi.
7 But if you answer me by saying: ‘We trust in the Lord our God.’ Is it not his high places and altars that Hezekiah has taken away? And he has said to Judah and to Jerusalem, ‘You shall worship before this altar.’
Kuma in ka ce mini, “Mun dogara ga Ubangiji Allahnmu ne” ba shi ba ne Hezekiya ya rurrushe masujadan kan tudunsa da bagadansa, yana ce wa Yahuda da Urushalima, “Dole ku yi sujada wa gaban wannan bagade”?
8 And now, hand yourselves over to my lord, the king of the Assyrians, and I will give you two thousand horses, and you will not be able to find riders for them on your own.
“‘Yanzu fa, bari in yi ciniki da maigidana, sarki Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sa mahaya a kansu!
9 So how will you withstand the face of the ruler of even one place, of even the least of my lord’s subordinates? But if you trust in Egypt, in four-horse chariots and in horsemen:
Yaya za ka ƙi hafsan mafi ƙanƙanci na hafsoshin maigidana, ko da yake kana dogara ga Masar don kekunan yaƙi da mahayan dawakai?
10 do I intend to go up against this land to destroy it without the Lord? But the Lord said to me, ‘Go up against this land, and destroy it.’”
Ban da haka kuma, na zo ne in faɗa in kuma hallaka wannan ƙasa ba tare da Ubangiji ba? Ubangiji kansa ya faɗa mini in tasar wa wannan ƙasa in kuma hallaka ta.’”
11 And Eliakim, and Shebna, and Joah said to Rabshakeh: “Speak to your servants in the Syrian language. For we understand it. Do not speak to us in the Jewish language, in the hearing of the people, who are upon the wall.”
Sai Eliyakim, Shebna da Yowa suka ce wa sarkin yaƙin, “Ka yi haƙuri ka yi wa bayinka magana da Arameyanci, da yake muna jinsa. Kada ka yi mana magana da Yahudanci a kunnen mutanen da suke kan katanga.”
12 And Rabshakeh said to them: “Has my lord sent me to your lord and to you in order to speak all these words, and not even more so to the men who are sitting on the wall, so that they may eat their own dung and drink their own urine with you?”
Amma sarkin yaƙin ya amsa ya ce, “Kuna tsammani ga maigidanku da ku ne kawai maigidana ya aiko ni in yi waɗannan maganganu, ba ga mutanen da suke zama a kan katanga ba, waɗanda kamar ku, za su ci kashinsu su kuma sha fitsarinsu?”
13 Then Rabshakeh stood up, and he cried out with a loud voice in the Jewish language, and he said: “Listen to the words of the great king, the king of the Assyrians.
Sa’an nan sarkin yaƙin ya tsaya ya kuma yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji kalmomin babban sarki, sarkin Assuriya!
14 Thus says the king: Do not let Hezekiah deceive you. For he will not be able to rescue you.
Ga abin da sarki ya ce kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku. Ba zai cece ku ba!
15 And do not let Hezekiah cause you to trust in the Lord, saying: ‘The Lord will rescue and free us. This city will not be given into the hands of the king of the Assyrians.’
Kada ku bar Hezekiya ya rarashe ku ku dogara ga Ubangiji sa’ad da ya ce, ‘Tabbatacce Ubangiji zai cece mu; ba za a ba da wannan birni a hannun sarkin Assuriya ba.’
16 Do not listen to Hezekiah. For the king of the Assyrians says this: Act with me to your own benefit, and come out to me. And let each one eat from his own vine, and each one from his own fig tree. And let each one drink water from his own well,
“Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya faɗa. Ku nemi salama da ni ku kuma fito zuwa wurina. Ta haka kowa zai ci daga kuringarsa da kuma itacen ɓaurensa ya kuma sha ruwa daga tankinsa,
17 until I arrive and take you away to a land which is like your own: a land of grain and of wine, a land of bread and of vineyards.
sai na zo na kuma kwashe ku zuwa ƙasa kamar taku, ƙasar hatsi da kuma sabon ruwan inabi, ƙasar abinci da gonakin inabi.
18 But you should not let Hezekiah disturb you, saying, ‘The Lord will deliver us.’ Have any of the gods of each of the nations delivered their land from the hand of the king of the Assyrians?
“Kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’ Allahn wata al’umma ya taɓa ceci ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
19 Where is the god of Hamath and of Arpad? Where is the god of Sepharvaim? Have they freed Samaria from my hand?
Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim? Sun fanshi Samariya daga hannuna?
20 Who is there, among all the gods of these lands, who has rescued his land from my hand, so that the Lord would rescue Jerusalem from my hand?”
Wanne cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa daga gare ni? Yaya kuwa Ubangiji zai iya ceci Urushalima daga hannuna?”
21 And they remained silent and did not answer a word to him. For the king had commanded them, saying, “You shall not respond to him.”
Amma mutanen suka yi shiru ba su kuwa ce kome ba, gama sarki ya yi umarni cewa, “Kada ku amsa masa.”
22 And Eliakim, son of Hilkiah, who was over the house, and Shebna, the scribe, and Joah, son of Asaph, the historian, entered to Hezekiah with their garments rent, and they reported to him the words of Rabshakeh.
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, Shebna magatakarda, da kuma Yowa ɗan Asaf marubuci suka tafi wurin Hezekiya, da rigunansu a kyakkece, suka kuwa faɗa masa abin da sarkin yaƙin ya yi ta farfaɗa.

< Isaiah 36 >