< Isaiah 34 >

1 O nations and peoples: draw near, and listen, and pay attention! Let the earth and its fullness hear, the entire world and all its offspring.
Ku zo kusa, ku al’ummai, ku kuwa saurara ku kasa kunne, ku mutane! Bari duniya ta ji, da kuma dukan abin da yake cikinta, duniya, da dukan abin da yake fitowa daga gare ta!
2 For the indignation of the Lord is over all the nations, and his fury is over all their armies. He has put them to death, and he has given them over to slaughter.
Ubangiji yana fushi da dukan al’ummai; hasalarsa tana a kan mayaƙansu. Zai hallaka su tas, zai ba da su a karkashe.
3 Their slain will be cast out, and from their carcasses a foul odor will rise up. The mountains will languish because of their blood.
Za a jefar da waɗanda aka kashe gawawwakinsu za su yi wari; duwatsu za su jiƙu da jininsu.
4 And the entire army of the heavens will languish, and the heavens will be folded like a book. And their entire army will fall away, as a leaf falls from the vine or from the fig tree.
Za a tumɓuke dukan taurarin sammai za a kuma nannaɗe sararin sama kamar littafi; dukan rundunar sama za su fāffāɗi kamar ganyayen da suka yanƙwane daga kuringa, kamar’ya’yan ɓauren da suka bushe daga itacen ɓaure.
5 “For my sword in heaven has been inebriated. Behold, it will descend upon Idumea, and upon the people of my slaughter, unto judgment.”
Takobina ya sha zararsa a cikin sammai; duba, ya sauko cikin hukunci a kan Edom, mutanen da zan hallaka tas.
6 The sword of the Lord has been filled with blood. It has been thickened by the blood of lambs and he-goats, by the innermost blood of rams. For the victim of the Lord is in Bozrah, and a great slaughter is in the land of Edom.
Takobin Ubangiji ya jiƙu da jini, ya rufu da kitse, jinin raguna da na awaki, kitse daga ƙodar raguna. Gama Ubangiji ya yi hadayar Bozra da kuma babban kisa a Edom.
7 And the single-horned beasts will descend with them, and the bulls along with the mighty. Their land will be inebriated by blood, and their ground by the fat of their lazy ones.
Babban bijimin jeji zai fāɗi tare da su, maruƙan bijimi da manyan bijimai. Ƙasarsu za tă cika da jini, ƙura kuma zai cika da kitse.
8 For this is the day of the vengeance of the Lord, the year of retribution for the judgment of Zion.
Gama Ubangiji yana da ranar ɗaukar fansa, shekarar ramuwa, don biya wa Sihiyona bukata.
9 And its torrents will be turned into tar, and its soil into sulfur. And its land will become burning tar.
Za a mai da rafuffukan Edom rami, ƙurarta za tă zama kibiritun farar wuta; ƙasarta za tă zama rami mai ƙuna!
10 Night and day, it will not be extinguished; its smoke will rise up without ceasing. From generation to generation it will remain desolate. No one will pass through it, forever and ever.
Ba za a kashe ta ba dare da rana; hayaƙinta za tă yi ta tashi har abada. Daga tsara zuwa tsara za tă zama kango; babu wani da zai ƙara wucewa ta wurin.
11 The pelican and the hedgehog will possess it. And the ibis and the raven will live in it. And a measuring line will be extended over it, so that it may be reduced to nothing, and a plumb line, unto desolation.
Mujiyar hamada da mujiya mai kuka za su mallake ta; babban mujiya da hankaka za su yi sheƙa a can. Allah zai miƙe a kan Edom magwajin bala’i da ma’aunin kango.
12 Its nobles will not be in that place. Instead, they will call upon the king, and all its leaders will be as nothing.
Sarakunanta ba za su kasance da wani abin da ake kira masarauta ba, dukan sarakunanta za su ɓace.
13 And thorns and nettles will rise up in its houses, and the thistle in its fortified places. And it will be the lair of serpents and the pasture of ostriches.
Ƙayayuwa za su mamaye fadodinta ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya za su cika kagaranta. Za tă zama mazaunin diloli da gida don mujiyoyi.
14 And demons and monsters will meet, and the hairy ones will cry out to one another. There, the ogress has lain down and found rest for herself.
Halittun hamada za su sadu da kuraye, awakin jeji za su yi ta kiran juna; a can halittun dare su ma za su huta su kuma nemi wurin hutu wa kansu.
15 In that place, the hedgehog has kept its den, and has raised its young, and has dug around them, and has kept them warm in its shadow. In that place, the birds of prey have joined together, one to another.
Mujiya za tă yi sheƙa a can ta zuba ƙwai; za tă ƙyanƙyashe su, ta kuma kula da’ya’yanta a inuwar fikafikanta; a can kuma shirwa za su taru, kowa da abokinsa.
16 Search and read diligently in the book of the Lord. Not one of them was lacking; not one has sought for the other. For what has proceeded from my mouth, he has commanded, and his very Spirit has gathered them.
Duba a cikin littafin Ubangiji ka kuma karanta. Babu wani a cikin waɗannan da ya ɓace, babu ko ɗaya da ba ta da abokiya. Gama bakinsa ne ya ba da umarni, Ruhunsa kuma zai tara su wuri ɗaya.
17 And he has cast lots over them. And his hand has distributed this to them by measure. They will possess it, even unto eternity. From generation to generation, they will dwell in it.
Ya ba su rabonsu; hannunsa ya rarraba musu ta wurin awo. Za su mallake ta har abada su kuma zauna a can daga tsara zuwa tsara.

< Isaiah 34 >