< Isaiah 32 >

1 Behold, the king will reign in justice, and the princes will rule in judgment.
Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
2 And a man will be like someone hidden from the wind, who conceals himself from a storm, or like rivers of waters in a time of thirst, or like the shadow of a rock that juts out in a desert land.
Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
3 The eyes of those who see will not be obscured, and the ears of those who hear will listen closely.
Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
4 And the heart of the foolish will understand knowledge, and the tongue of those with impaired speech will speak quickly and plainly.
Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
5 He who is foolish will no longer be called leader, nor will the deceitful be called greater.
Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
6 For a foolish man speaks foolishness and his heart works iniquity in order to accomplish deception. And he speaks to the Lord deceitfully, so as to empty the soul of the hungry and to take away drink from the thirsty.
Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
7 The tools of the deceitful are very wicked. For they have concocted plans to destroy the meek by lying words, though the poor speak judgment.
Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
8 Yet truly, the prince will plan things that are worthy of a prince, and he will stand above the rulers.
Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
9 You opulent women, rise up and listen to my voice! O confident daughters, play close attention to my eloquence!
Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
10 For after a year and some days, you who are confident will be disturbed. For the vintage has been completed; the gathering will no longer occur.
Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
11 Be stupefied, you opulent women! Be disturbed, O confident ones! Strip yourselves, and be confounded; gird yourselves at the waist.
Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
12 Mourn over your breasts, over the delightful country, over the fruitful vineyard.
Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
13 Thorn and brier will rise up, over the soil of my people. How much more over all the houses of gladness, over the city of exultation?
da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
14 For the house has been forsaken. The multitude of the city has been abandoned. A darkness and a covering have been placed over its dens, even unto eternity. It will be the gladness of wild donkeys and the pasture of flocks,
Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
15 until the Spirit is poured over us from on high. And the desert will be a fruitful field, and the fruitful field will be considered as a forest.
sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
16 And judgment will live in solitude, and justice will be seated in a fruitful place.
Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
17 And the work of justice will be peace. And the service of justice will be quiet and secure, forever.
Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
18 And my people will be seated in the beauty of peacefulness, and in the tabernacles of faithfulness, and in the opulence of restfulness.
Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
19 But hail will be in the descent of the forest, and the city will be brought exceedingly low.
Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
20 Blessed are you who sow over any waters, sending the feet of the ox and the donkey there.
zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.

< Isaiah 32 >