< Isaiah 14 >

1 Her time is drawing near, and her days will not be prolonged. For the Lord will take pity on Jacob, and he will still choose from Israel, and he will cause them to rest upon their own soil. And the new arrival will be joined to them, and he will adhere to the house of Jacob.
Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
2 And the people will take them, and lead them to their place. And the house of Israel will possess them, in the land of the Lord, as men and women servants. And they will take captive those who had taken them captive. And they will subjugate their oppressors.
Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
3 And this shall be in that day: when God will have given you rest from your labor, and from your oppression, and from the difficult servitude under which you served before,
A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
4 you will accept this parable against the king of Babylon, and you will say: “How is it that the oppressor has ceased, along with his tribute?
za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
5 The Lord has crushed the staff of the impious, the scepter of despots,
Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
6 which struck the people in wrath with an incurable wound, which subjugated the nations in fury, which persecuted with cruelty.
wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
7 All the earth has become quiet and still; it has been gladdened and has rejoiced.
Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
8 The evergreens, too, have rejoiced over you, and the cedars of Lebanon, saying: ‘Since you have slept, no one has ascended who would cut us down.’
Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
9 Hell below was stirred up to meet you at your advent; it has awakened the giants for you. All the leaders of the earth have risen from their thrones, all the leaders among the nations.” (Sheol h7585)
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
10 Everyone will respond and will say to you: “Now you are wounded, just as we were; you have become like us.
Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
11 Your arrogance has been dragged down to Hell. Your body has fallen dead. The moths will be strewn beneath you, and the worms will be your covering. (Sheol h7585)
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
12 How is it that you have fallen from heaven, O Lucifer, who used to rise like the sun? How is it that you have fallen to the earth, you who wounded the peoples?
Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
13 And you said in your heart: ‘I will climb up to heaven. I will exalt my throne above the stars of God. I will be enthroned upon the mountain of the covenant, on the northern parts.
Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
14 I will ascend above the tops of the clouds. I will be like the Most High.’
Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
15 Yet truly, you shall be dragged down to Hell, into the depths of the pit. (Sheol h7585)
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
16 Those who see you, will lean toward you, and will gaze upon you, saying: ‘Could this be the man who disturbed the earth, who shook kingdoms,
Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
17 who made the world into a desert and destroyed its cities, who would not even open a prison for his prisoners?’”
mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
18 All the kings of the nations throughout the whole world have slept in glory, each man in his own house.
Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
19 But you have been rejected from your grave, like a useless polluted plant, and you have been bound up with those who were slain by the sword, and who descended to the bottom of the pit, like a rotting carcass.
Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
20 You will not be associated with them, even in the grave. For you have destroyed your own land; you have slain your own people. The offspring of the wicked ones will not be called upon for eternity.
ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
21 Prepare his sons for the slaughter, according to the iniquity of their fathers. They will not rise up, nor inherit the earth, nor fill the face of the world with cities.
A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
22 But I will rise up against them, says the Lord of hosts. And I will perish the name of Babylon and its remnants: both the plant and its progeny, says the Lord.
“Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
23 And I will appoint it as a possession for the hedgehog, with swamps of water. And I will sweep it out and wear it away with a brush, says the Lord of hosts.
“Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
24 The Lord of hosts has sworn, saying: Surely, just as I have considered it, so shall it be, and in the same manner as I have drawn it through my mind,
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
25 so shall it occur. So shall I crush the Assyrian in my land, and I will trample him upon my mountains, and his yoke will be taken away from them, and his burden will be removed from their shoulder.
Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
26 This is the plan that I have decided, concerning the entire earth, and this is the hand which is extended over all the nations.
Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
27 For the Lord of hosts has decreed it, and who is able to weaken it? And his hand is extended, so who can avert it?
Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
28 In the year in which king Ahaz died, this burden was given:
Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
29 You should not rejoice, all you of Philistia, that the rod of him who struck you has been crushed. For from the root of the serpent will go forth a king snake, and his offspring will engulf that which flies.
Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
30 And the firstborn of the poor will be pastured, and the poor will rest in faithfulness. And I will cause your root to pass away by famine, and I will put to death your remnant.
Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
31 Wail, O gate! Cry out, O city! All of Philistia has been prostrated. For a smoke will arrive from the north, and there is no one who will escape his army.
Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
32 And what will be the response to this news among the nations? It will be that the Lord has established Zion, and that the poor of his people will hope in him.
Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”

< Isaiah 14 >