< Isaiah 13 >

1 The burden of Babylon which Isaiah, the son of Amoz, saw.
Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
2 Over the foggy mountain lift up a sign! Raise the voice, lift up the hand, and let the rulers enter through the gates!
A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
3 In my wrath, I commanded my sanctified ones, and I called my strong ones, those who exult in my glory.
Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
4 On the mountains, there is the voice of a multitude, as if of a numerous people, a voice with the sound of kings, of nations gathered together. For the Lord of hosts has given orders to soldiers of war,
Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
5 to those who are arriving from a far off land, from the heights of the heavens. It is the Lord and the instruments of his fury, so that he may bring ruin to all the earth.
Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
6 Wail aloud! For the day of the Lord draws near! It will arrive like a devastation from the Lord.
Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
7 Because of it, every hand will fail, and every heart of man will waste away and be crushed.
Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
8 Writhing and pain will seize them. They will be in pain, like a woman in labor. Each one will appear stupefied to his neighbor. Their countenances will be like faces which have been burned up.
Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
9 Behold, the day of the Lord approaches: a cruel day, full of indignation and wrath and fury, which will place the earth in solitude and crush the sinners from it.
Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
10 For the stars of the heavens, in their splendor, will not display their light. The sun will be obscured at its rising, and the moon will not shine in her brightness.
Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
11 And I will act against the evils of the world, and against the impious for their iniquity. And I will cause the pride of the unfaithful to cease, and I will bring down the arrogance of the strong.
Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
12 A man will be more precious than gold, and mankind will become like pure refined gold.
Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
13 For this purpose, I will stir up heaven, and the earth will be moved from its place, because of the indignation of the Lord of hosts, because of the day of his furious wrath.
Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
14 And they will be like a doe fleeing away, or like sheep; and there will be no one who may gather them together. Each one will turn to his own people, and every one will flee to his own land.
Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
15 All who are found will be killed, and all who are caught unaware will fall by the sword.
Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
16 Their infants will be thrown down violently before their eyes. Their houses will be plundered, and their wives will be violated.
Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
17 Behold, I will stir up the Medes against them. They will not seek silver, nor desire gold.
Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
18 Instead, with their arrows, they will put the little children to death, and they will take no pity on breastfeeding women, and their eye will not spare their children.
Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
19 And then Babylon, the glorious one among kingdoms, that famous pride of the Chaldeans, will be destroyed, even as the Lord destroyed Sodom and Gomorrah.
Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
20 It will not be inhabited, even unto the end, and it will not be reestablished, even from generation to generation. The Arab will not pitch his tents there, nor will the shepherds take rest there.
Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
21 Instead, the wild beasts will rest there, and their houses will be filled with serpents, and ostriches will live there, and the hairy ones will leap about there.
Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
22 And the tawny owls will answer one another there, in its buildings, and the Sirens in its shrines of pleasure.
Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.

< Isaiah 13 >