< Isaiah 12 >

1 And you will say in that day: “I will confess to you, O Lord, because you have been angry with me; but your fury has been turned away, and you have consoled me.
A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
2 Behold, God is my savior, I will act faithfully, and I will not be afraid. For the Lord is my strength and my praise, and he has become my salvation.”
Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
3 You will draw water with gladness from the fountains of the Savior.
Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
4 And you will say in that day: “Confess the Lord, and invoke his name! Make his plans known among the peoples! Remember that his name is exalted!
A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
5 Sing to the Lord, for he has acted magnificently! Announce it to the whole world!
Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
6 Exult and give praise, O habitation of Zion! For the Great One, the Holy One of Israel, is in your midst!”
Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”

< Isaiah 12 >