< Isaiah 10 >

1 Woe to those who make unfair laws, and who, when writing, write injustice:
Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
2 in order to oppress the poor in judgment, and to do violence to the case of the humble of my people, in order that widows may be their prey, and that they might plunder the orphan.
don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
3 What will you do on the day of visitation and calamity which is approaching from afar? To whom will you flee for assistance? And where will you leave behind your own glory,
Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
4 so that you may not be bowed down under the chains, and fall with the slain? Concerning all this, his fury was not turned away; instead, his hand was still extended.
Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
5 Woe to Assur! He is the rod and the staff of my fury, and my indignation is in their hands.
“Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
6 I will send him to a deceitful nation, and I will order him against the people of my fury, so that he may take away the plunder, and tear apart the prey, and place it to be trampled like the mud of the streets.
Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
7 But he will not consider it to be so, and his heart will not suppose it to be this way. Instead, his heart will be set to crush and to exterminate more than a few nations.
Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
8 For he will say:
Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
9 “Are not my princes like many kings? Is not Calno like Carchemish, and Hamath like Arpad? Is not Samaria like Damascus?
‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
10 In the same manner as my hand reached the kingdoms of the idol, so also will it reach their false images, those of Jerusalem and of Samaria.
Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
11 Should I not do to Jerusalem and her false images, just as I have done to Samaria and her idols?”
ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
12 And this shall be: when the Lord will have completed each of his works on Mount Zion and in Jerusalem, I will act against the fruit of the exalted heart of king Assur, and against the glory of the haughtiness of his eyes.
Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
13 For he has said: “I have acted with the strength of my own hand, and I have understood with my own wisdom, and I have removed the limits of the people, and I have plundered their leaders, and, like one with power, I have pulled down those residing on high.
Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
14 And my hand has reached to the strength of the people, as to a nest. And, just as the eggs which have been left behind are gathered, so have I gathered the entire earth. And there was no one who moved a wing, or opened a mouth, or uttered a snarl.”
Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
15 Should the axe glorify itself over him who wields it? Or can the saw exalt itself over him who pulls it? How can a rod lift itself up against him who wields it, or a staff exalt itself, though it is only wood?
Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
16 Because of this, the sovereign Lord, the Lord of hosts, will send leanness among his fat ones. And under the influence of his glory, a burning ardor will rage, like a consuming fire.
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
17 And the light of Israel will be like a fire, and the Holy One of Israel will be like a flame. And his thorns and briers will be set ablaze and devoured, in one day.
Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
18 And the glory of his forest and of his beautiful hill will be consumed, from the soul even to the flesh. And he will flee away in terror.
Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
19 And what remains of the trees of his forest will be so few, and so easily numbered, that even a child could write them down.
Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
20 And this shall be in that day: those not added to the remnant of Israel, and those who escape of the house of Jacob, will not lean upon him who strikes them. Instead, they will lean upon the Lord, the Holy One of Israel, in truth.
A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
21 The remnant of Jacob, again I say the remnant, will be converted to the mighty God.
Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
22 For though your people, O Israel, will be like the sand of the sea, yet only a remnant of them will be converted. The consummation, having been shortened, will be inundated with justice.
Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
23 For the Lord, the God of hosts, will accomplish an abbreviation and a consummation, in the midst of all the earth.
Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
24 For this reason, the Lord, the God of hosts, says this: “My people, who inhabit Zion: do not be afraid of Assur. He will strike you with his rod, and he will lift up his staff over you, on the way of Egypt.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
25 But after a little while and a brief time, my indignation will be consumed, and my fury will turn to their wickedness.”
Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
26 And the Lord of hosts will raise up a scourge over him, like the scourge of Midian at the rock of Oreb, and he will raise up his rod over the sea, and he will lift it up against the way of Egypt.
Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
27 And this shall be in that day: his burden will be taken away from your shoulder, and his yoke will be taken away from your neck, and the yoke will decay at the appearance of the oil.
A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
28 He will approach Aiath; he will cross into Migron; he will entrust his vessels to Michmash.
Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
29 They have passed through in haste; Geba is our seat; Ramah was stupefied; Gibeah of Saul fled.
Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
30 Neigh with your voice, daughter of Gallim; pay attention, Laishah, impoverished woman of Anathoth.
Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
31 Madmenah has moved away; be strengthened, you inhabitants of Gebim.
Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
32 It is still daylight, so stand at Nob. He will shake his hand against the mountain of the daughter of Zion, the hill of Jerusalem.
A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
33 Behold, the sovereign Lord of hosts will crush the little bottle of wine with terror, and the exalted in stature will be cut down, and the lofty will be brought low.
Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
34 And the dense forest will be overturned with iron. And Lebanon, with its exalted ones, will fall.
Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.

< Isaiah 10 >