< Hosea 3 >

1 And the Lord said to me: “Go yet again, and love a woman, beloved by a friend, yet an adulteress, for so does the Lord love the sons of Israel, yet they look to strange gods, and love the seeds of grapes.”
Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi, ka sāke nuna wa matarka ƙauna, ko da yake wani yana son ta, ita kuma mazinaciya ce. Ka ƙaunace ta yadda Ubangiji yake ƙaunar Isra’ilawa, ko da yake sun juya ga waɗansu alloli suna kuma ƙauna wainar zabibi mai tsarki.”
2 And I contracted her to me for fifteen silver coins, and for a basket of barley, and half a basket of barley.
Ta haka na saye ta da shekel goma sha biyar na azurfa da kuma wajen buhu na sha’ir.
3 And I said to her, “You will wait for me for many days. You will not commit fornication, and you will not be with a man. But I also will wait for you.”
Sai na faɗa mata, “Za ki zauna tare da ni kwanaki masu yawa; kada ki yi karuwanci ko ki yi abuta da wani namiji, ni kuwa zan zauna tare da ke.”
4 For the sons of Israel will sit for many days without a king, and without a leader, and without sacrifice, and without altar, and without priestly vestments, and without religious symbols.
Gama Isra’ilawa za su yi kwanaki masu yawa ba tare da sarki ko shugaba ba, babu hadaya ko keɓaɓɓun duwatsu, babu efod ko gunki.
5 And after this, the sons of Israel will return, and they will seek the Lord their God and David their king, and they will be terrified by the Lord and by his goodness, in the last days.
Daga baya Isra’ilawa za su dawo su nemi Ubangiji Allahnsu da kuma Dawuda sarkinsu. Za su je da rawan jiki wajen Ubangiji da kuma ga albarkunsa a kwanakin ƙarshe.

< Hosea 3 >