< Haggai 2 >

1 And in the seventh month, on the twenty-first of the month, the word of the Lord came, by the hand of Haggai the prophet, saying:
a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
2 Speak to Zerubbabel the son of Shealtiel, the governor of Judah, and to Jesus the son of Jehozadak, the high priest, and to the remainder of the people, saying:
“Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
3 Who is left among you, who saw this house in its first glory? And how do you see it now? Is it not, in comparison to that, as nothing in your eyes?
‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
4 And now be strengthened, Zerubbabel, says the Lord. And be strengthened, Jesus the son of Jehozadak, the high priest. And be strengthened, all people of the land, says the Lord of hosts. For I am with you, says the Lord of hosts.
Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
5 And act according to the word that I planted with you when you departed from the land of Egypt. And my Spirit will be in your midst. Do not be afraid.
‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
6 For thus says the Lord of hosts: There is yet one brief time, and I will move heaven and earth, and the sea and the dry land.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
7 And I will move all nations. And the Desired of all nations will arrive. And I will fill this house with glory, says the Lord of hosts.
Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
8 Mine is the silver, and mine is the gold, says the Lord of hosts.
‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 Great shall be the glory of this house, the last more than the first, says the Lord of hosts. And in this place, I will bestow peace, says the Lord of hosts.
‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
10 On the twenty-fourth of the ninth month, in the second year of king Darius, the word of the Lord came to Haggai the prophet, saying:
A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
11 Thus says the Lord of hosts: the priests question the law, saying:
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
12 If a man will have carried sanctified flesh in the pocket of his garment, and the top of it touches his bread, or appetizer, or wine, or oil, or any food, shall it be sanctified? But the priests responded by saying, “No.”
Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
13 And Haggai said, “If the polluted in soul will have touched any of all these things, shall it be contaminated?” And the priests responded and said, “It shall be contaminated.”
Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
14 And Haggai answered and he said: Such is this people, and such is this nation before my face, says the Lord, and such is all the work of their hands. And so all that they have offered there has been contaminated.
Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
15 And now, consider in your hearts, from this day and beyond, before stone may be placed upon stone in the temple of the Lord:
“‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
16 when you approached a pile of twenty measures, and they became ten, and you entered to the press, to press out fifty bottles, and they became twenty,
A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
17 how I struck you with a burning wind, and a mildew, and a hailstorm, all the works of your hand, yet there was no one among you who returned to me, says the Lord.
Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
18 Set your hearts from this day and into the future, from the twenty-fourth day of the ninth month, from the day that the foundations of the temple of the Lord have been uttered, and place it upon your heart.
‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
19 Has the seed been germinated yet? And has the vine, and the fig tree, and the pomegranate, and the olive tree still not flourished? From this day on, I will bless you.
Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
20 And the word of the Lord came a second time to Haggai, on the twenty-fourth of the month, saying:
Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
21 Speak to Zerubbabel the governor of Judah, saying: I will move both heaven and earth.
“Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
22 And I will overturn the throne of kingdoms, and I will crush the strength of the kingdom of the Gentiles. And I will overturn the four-horse chariot, and its rider; and the horses and their riders shall be brought down, a man by the sword of his brother.
Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
23 In that day, says the Lord of hosts, I will take you, Zerubbabel the son of Shealtiel, my servant, says the Lord, and will set you like a seal, for I have chosen you, says the Lord of hosts.
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”

< Haggai 2 >