< Habakkuk 3 >

1 A Prayer of Habakkuk the Prophet on Behalf of Those Who Are Ignorant.
Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
2 Lord, I heard what has been said about you, and I was afraid. Lord, your work, in the midst of years, revive it. In the midst of years, you will make it known. When you have become angry, you will remember mercy.
Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
3 God will come from the south, and the Holy One from mount Pharan. His glory has covered the heavens, and the earth is full of his praise.
Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
4 His brightness shall be like the light; horns are in his hands. There, his strength has been hidden.
Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
5 Death will go forth before his face. And the devil shall depart before his feet.
Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
6 He stood, and measured the earth. He looked, and dissolved the Gentiles. And the mountains of ages past have been shattered. The hills of the world became curved by the journeys of his eternity.
Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
7 I saw the tents of Ethiopia for their iniquity; the tent-skins of the land of Midian will be thrown into confusion.
Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
8 Could you have been angry with the rivers, Lord? Or was your fury within the rivers, or your indignation in the sea? He will ascend upon your horses, and your four-horse chariots are salvation.
Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
9 Being stirred up, you will take up your bow, the oaths you have spoken to the tribes. You will split apart the Rivers of the earth.
Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
10 They saw you, and the mountains grieved. The great body of waters crossed over. The abyss uttered its voice. The pinnacle lifted up its hands.
duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
11 The sun and the moon have stood firm in their dwelling place; with the light of your arrows, they shall go forth in the splendor of your flashing spear.
Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
12 With a roar, you will trample the earth. In your fury, you will cause the nations to be stupefied.
Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
13 You have gone forth for the salvation of your people, for salvation with your Christ. You struck the head of the house of the impious. You have laid bare his foundation all the way to the neck.
Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
14 You have cursed his scepters, the head of his warriors, those who approached like a whirlwind so as to scatter me. Their exultation was like one who devours the poor in secret.
Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
15 You made a way in the sea for your horses, in the mud of great waters.
Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
16 I heard, and my stomach became troubled. My lips trembled at the voice. Let decay enter into my bones and gush forth from within me. Then I may rest in the day of tribulation, so that I may ascend to our people well-prepared.
Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
17 For the fig tree will not flower, and there will be no bud on the vines. The labor of the olive tree will be misleading, and the farmland will produce no food. The sheep will be cut off from the sheepfold, and there will be no herd at the manger.
Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
18 But I will rejoice in the Lord; and I will exult in God my Jesus.
duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
19 The Lord God is my strength. And he will set my feet like those of the stag. And he, the victor, will lead me beyond my high places while singing psalms.
Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi.

< Habakkuk 3 >