+ Genesis 1 >

1 In the beginning, God created heaven and earth.
A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
2 But the earth was empty and unoccupied, and darknesses were over the face of the abyss; and so the Spirit of God was brought over the waters.
To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
3 And God said, “Let there be light.” And light became.
Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.
4 And God saw the light, that it was good; and so he divided the light from the darknesses.
Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
5 And he called the light, ‘Day,’ and the darknesses, ‘Night.’ And it became evening and morning, one day.
Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
6 God also said, “Let there be a firmament in the midst of the waters, and let it divide waters from waters.”
Allah ya ce, “Bari sarari yă kasance tsakanin ruwaye domin yă raba ruwa da ruwa.”
7 And God made a firmament, and he divided the waters that were under the firmament, from those that were above the firmament. And so it became.
Saboda haka Allah ya yi sarari ya raba ruwan da yake ƙarƙashin sararin da ruwan da yake bisansa. Haka kuwa ya kasance.
8 And God called the firmament ‘Heaven.’ And it became evening and morning, the second day.
Allah ya kira sararin “sama.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyu ke nan.
9 Truly God said: “Let the waters that are under heaven be gathered together into one place; and let the dry land appear.” And so it became.
Allah ya ce, “Bari ruwan da yake ƙarƙashin sama yă tattaru wuri ɗaya, bari kuma busasshiyar ƙasa tă bayyana.” Haka kuwa ya kasance.
10 And God called the dry land, ‘Earth,’ and he called the gathering of the waters, ‘Seas.’ And God saw that it was good.
Allah ya kira busasshiyar ƙasar “doron ƙasa,” ruwan da ya taru kuma, ya kira “tekuna.” Allah ya ga yana da kyau.
11 And he said, “Let the land spring forth green plants, both those producing seed, and fruit-bearing trees, producing fruit according to their kind, whose seed is within itself, over all the earth.” And so it became.
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari ƙasa tă fid da tsire-tsire, da shuke-shuke, da itatuwa a bisa ƙasa masu ba da amfani da’ya’ya a cikinsu, bisa ga irinsu.” Haka kuwa ya kasance.
12 And the land brought forth green plants, both those producing seed, according to their kind, and trees producing fruit, with each having its own way of sowing, according to its species. And God saw that it was good.
Ƙasar ta fid da tsire-tsire, da shuke-shuke masu ba da’ya’ya bisa ga irinsu, ta fid kuma da itatuwa masu ba da’ya’ya da iri a cikinsu bisa ga irinsu. Allah ya ga yana da kyau.
13 And it became evening and the morning, the third day.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta uku ke nan.
14 Then God said: “Let there be lights in the firmament of heaven. And let them divide day from night, and let them become signs, both of the seasons, and of the days and years.
Allah kuma ya ce, “Bari haskoki su kasance a sararin sama domin su raba yini da dare, bari su zama alamu domin su nuna yanayi, da ranaku, da kuma shekaru,
15 Let them shine in the firmament of heaven and illuminate the earth.” And so it became.
bari kuma haskokin su kasance a sararin sama domin su ba da haske a duniya.” Haka kuwa ya kasance.
16 And God made two great lights: a greater light, to rule over the day, and a lesser light, to rule over the night, along with the stars.
Allah ya yi manyan haskoki biyu, babban hasken yă mallaki yini, ƙaramin kuma yă mallaki dare. Ya kuma yi taurari.
17 And he set them in the firmament of heaven, to give light over all the earth,
Allah ya sa su a sararin sama domin su ba da haske a duniya,
18 and to rule over the day as well as the night, and to divide light from darkness. And God saw that it was good.
su mallaki yini da kuma dare, su kuma raba haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
19 And it became evening and morning, the fourth day.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta huɗu ke nan.
20 And then God said, “Let the waters produce animals with a living soul, and flying creatures above the earth, under the firmament of heaven.”
Allah ya ce, “Bari ruwa yă cika da halittu masu rai, bari tsuntsaye kuma su tashi sama a bisa duniya a sararin sama.”
21 And God created the great sea creatures, and everything with a living soul and the ability to move that the waters produced, according to their species, and all the flying creatures, according to their kind. And God saw that it was good.
Allah ya halicci manyan halittun teku, da kowane mai rai da abin da yake motsi a ruwa, bisa ga irinsu, da kuma kowane tsuntsu mai fiffike bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
22 And he blessed them, saying: “Increase and multiply, and fill the waters of the sea. And let the birds be multiplied above the land.”
Allah ya albarkace su ya ce, “Ku yi ta haihuwa ku kuma ƙaru da yawa, ku cika ruwan tekuna, bari kuma tsuntsaye su yi yawa a bisa duniya.”
23 And it became evening and morning, the fifth day.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyar ke nan.
24 God also said, “Let the land produce living souls in their kind: cattle, and animals, and wild beasts of the earth, according to their species.” And so it became.
Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa tă ba da halittu masu rai bisa ga irinsu; dabbobi da halittu masu rarrafe, da kuma namun jeji, kowane bisa ga irinsa.” Haka kuwa ya kasance.
25 And God made the wild beasts of the earth according to their species, and the cattle, and every animal on the land, according to its kind. And God saw that it was good.
Allah ya halicci namun jeji bisa ga irinsu, dabbobi bisa ga irinsu, da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
26 And he said: “Let us make Man to our image and likeness. And let him rule over the fish of the sea, and the flying creatures of the air, and the wild beasts, and the entire earth, and every animal that moves on the earth.”
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, tsuntsayen sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
27 And God created man to his own image; to the image of God he created him; male and female, he created them.
Saboda haka Allah ya halicci mutum cikin siffarsa. Cikin kamannin Allah, Allah ya halicci mutum. Miji da mace ya halicce su.
28 And God blessed them, and he said, “Increase and multiply, and fill the earth, and subdue it, and have dominion over the fish of the sea, and the flying creatures of the air, and over every living thing that moves upon the earth.”
Allah ya albarkace su, ya kuma ce musu, “Ku yi ta haihuwa ku ƙaru da yawa, ku mamaye duniya, ku mallake ta. Ku yi mulki a bisa kifin teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma bisa kowace halitta mai rai wadda take rarrafe a ƙasa.”
29 And God said: “Behold, I have given you every seed-bearing plant upon the earth, and all the trees that have in themselves the ability to sow their own kind, to be food for you,
Sa’an nan Allah ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da’ya’ya masu kwaya da suke a fāɗin duniya, da dukan itatuwa masu ba da’ya’ya, don su zama abinci a gare ku.
30 and for all the animals of the land, and for all the flying things of the air, and for everything that moves upon the earth and in which there is a living soul, so that they may have these on which to feed.” And so it became.
Na kuma ba da dukan dabbobin ƙasa, da dukan tsuntsayen sama, da dukan abin da yake rarrafe a ƙasa, da dai iyakar abin da yake numfashi; haka kuma na ba da ganyaye su zama abinci.” Haka kuwa ya kasance.
31 And God saw everything that he had made. And they were very good. And it became evening and morning, the sixth day.
Allah ya ga dukan abin da ya yi, yana da kyau ƙwarai. Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta shida ke nan.

+ Genesis 1 >