< Genesis 8 >

1 Then God remembered Noah, and all living things, and all the cattle, which were with him in the ark, and he brought a wind across the earth, and the waters were diminished.
Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
2 And the fountains of the abyss and the floodgates of heaven were closed. And the rain from heaven was restrained.
Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
3 And the waters were restored to their coming and going from the earth. And they began to diminish after one hundred and fifty days.
Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
4 And the ark rested in the seventh month, on the twenty-seventh day of the month, upon the mountains of Armenia.
A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
5 Yet in truth, the waters were departing and decreasing until the tenth month. For in the tenth month, on the first day of the month, the tips of the mountains appeared.
Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
6 And when forty days had passed, Noah, opening the window that he had made in the ark, sent forth a raven,
Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
7 which went forth and did not return, until the waters were dried up across the earth.
ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
8 Likewise, he sent forth a dove after him, in order to see if the waters had now ceased upon the face of the earth.
Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
9 But when she did not find a place where her foot might rest, she returned to him in the ark. For the waters were upon the whole earth. And he extended his hand and caught her, and he brought her into the ark.
Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
10 And then, having waited a further seven days, he again sent forth the dove out of the ark.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
11 And she came to him in the evening, carrying in her mouth an olive branch with green leaves. Noah then understood that the waters had ceased upon the earth.
Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
12 And nevertheless, he waited another seven days. And he sent forth the dove, which no longer returned to him.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
13 Therefore, in the six hundred and first year, in the first month, on the first day of the month, the waters were diminished upon the earth. And Noah, opening the cover of the ark, gazed out and saw that the surface of the earth had become dry.
A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
14 In the second month, on the twenty-seventh day of the month, the earth was made dry.
A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
15 Then God spoke to Noah, saying:
Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
16 “Go out of the ark, you and your wife, your sons and the wives of your sons with you.
“Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
17 Bring out with you all the living things that are with you, all that is flesh: as with the birds, so also with the wild beasts and all the animals that move upon the earth. And enter upon the land: increase and multiply upon it.”
Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
18 And so Noah and his sons went out, and his wife and the wives of his sons with him.
Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
19 Then also all living things, and the cattle, and the animals that move upon the earth, according to their kinds, departed from the ark.
da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
20 Then Noah built an altar to the Lord. And, taking from each of the cattle and birds that were clean, he offered holocausts upon the altar.
Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
21 And the Lord smelled the sweet odor and said: “I will no longer curse the earth because of man. For the feelings and thoughts of the heart of man are prone to evil from his youth. Therefore, I will no longer pierce every living soul as I have done.
Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
22 All the days of the earth, seedtime and harvest, cold and heat, summer and winter, night and day, will not cease.”
“Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”

< Genesis 8 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark