< Genesis 6 >

1 And when men began to be multiplied upon the earth, and daughters were born to them,
Sa’ad da mutane suka fara ƙaruwa a duniya, aka kuma hahhaifi musu’ya’ya mata,
2 the sons of God, seeing that the daughters of men were beautiful, took to themselves wives from all whom they chose.
sai’ya’yan Allah maza suka ga cewa’ya’yan mutane mata suna da bansha’awa, sai suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura.
3 And God said: “My spirit shall not remain in man forever, because he is flesh. And so his days shall be one hundred and twenty years.”
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ruhuna ba zai zauna a cikin mutum har abada ba, saboda shi mai mutuwa ne, kwanakinsa za su zama shekaru ɗari da arba’in ne.”
4 Now giants were upon the earth in those days. For after the sons of God went in to the daughters of men, and they conceived, these became the powerful ones of ancient times, men of renown.
Nefilimawa suna nan a duniya a waɗancan kwanaki, da kuma kwanakin da suka bi baya, a sa’ad da’ya’yan Allah suka kwana da’ya’yan mutane mata, suka kuma hahhaifi musu’ya’ya. Ai, su ne jarumawan dā, mutanen da suka shahara.
5 Then God, seeing that the wickedness of men was great upon the earth and that every thought of their heart was intent upon evil at all times,
Ubangiji kuwa ya lura cewa muguntar mutum ta yi yawa a duniya, kuma kowane abin da yake tunani a zuciyarsa mugu ne kawai a kowanne lokaci.
6 repented that he had made man on the earth. And being touched inwardly with a sorrow of heart,
Ubangiji ya damu da ya yi mutum a duniya, abin ya zafe shi ƙwarai.
7 he said, “I will eliminate man, whom I have created, from the face of the earth, from man to other living things, from animals even to the flying things of the air. For it grieves me that I have made them.”
Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan kawar da mutum, da dabbobi, da halittu masu rarrafe a ƙasa da kuma tsuntsayen sama waɗanda na halitta, daga doron ƙasa, saboda na damu da na yi su.”
8 Yet truly, Noah found grace before the Lord.
Amma Nuhu ya sami tagomashi a gaban Ubangiji.
9 These are the generations of Noah. Noah was a just man, and yet he was predominate among his generations, for he walked with God.
Ga tarihin Nuhu. Nuhu mutum ne mai adalci, marar abin zargi a cikin mutanen zamaninsa, ya kuma yi tafiya tare da Allah.
10 And he conceived three sons: Shem, Ham, and Japheth.
Nuhu yana da’ya’ya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
11 Yet the earth was corrupted before the eyes of God, and it was filled with iniquity.
Duniya dai ta lalace sosai a gaban Allah, ta kuma cika da tashin hankali.
12 And when God had seen that the earth had been corrupted, (indeed, all flesh had corrupted its way upon the earth)
Allah ya ga yadda duniya ta lalace, gama dukan mutane a duniya sun lalatar da rayuwarsu.
13 he said to Noah: “The end of all flesh has arrived in my sight. The earth has been filled with iniquity by their presence, and I will destroy them, along with the earth.
Saboda haka, Allah ya ce wa Nuhu, “Zan kawo ƙarshen dukan mutane, gama saboda su duniya ta cika da tashin hankali. Lalle zan hallaka su da kuma duniya.
14 Make yourself an ark from smoothed wood. You shall make little dwelling places in the ark, and you shall smear pitch on the interior and exterior.
Saboda haka ka yi wa kanka jirgi da katakon Saifires, ka yi ɗakuna a cikinsa, ka shafe shi da ƙaro ciki da waje.
15 And thus shall you make it: The length of the ark shall be three hundred cubits, its width fifty cubits, and its height thirty cubits.
Ga yadda za ka gina shi; jirgin zai kasance mai tsawon ƙafa 45, fāɗinsa ƙafa 75, tsayinsa kuma ƙafa 45.
16 You shall make a window in the ark, and you shall complete it within a cubit of the top. Then you shall set the door of the ark at its side. You shall make in it: a lower part, upper rooms, and a third level.
Ka yi masa rufi, ka kuma ba da fili inci 18 tsakanin rufin a kowane gefen jirgin. Ka sa ƙofa a gefen jirgin. Ka yi shi hawa uku, ka yi ƙofa a gefe.
17 Behold, I shall bring the waters of a great flood upon the earth, so as to put to death all flesh in which there is the breath of life under heaven. All things that are on the earth shall be consumed.
Ga shi zan aiko da ambaliya ruwa a duniya, in hallaka dukan mai rai da yake a ƙarƙashin sama, kowace halittar da take numfashi a cikinta. Dukan abin da yake a duniya zai hallaka.
18 And I shall establish my covenant with you, and you shall enter the ark, you and your sons, your wife and the wives of your sons with you.
Amma zan kafa alkawarina da kai, kai kuma za ka shiga jirgin, kai da’ya’yanka maza da matarka da matan’ya’yanka tare da kai.
19 And from every living thing of all that is flesh, you shall lead pairs into the ark, so that they may survive with you: from the male sex and the female,
Za ka shigar da biyu na dukan halittu masu rai, namiji da ta mace a cikin jirgin, domin su rayu tare da kai.
20 from birds, according to their kind, and from beasts, in their kind, and from among all animals on earth, according to their kind; pairs from each shall enter with you, so that they may be able to live.
Biyu na kowane irin tsuntsu, kowace irin dabba da kuma kowace irin halitta mai rarrafe a ƙasa, za su zo wurinka domin a bar su da rai.
21 Therefore, you shall take with you from all the foods that are able to be eaten, and you shall carry these with you. And these shall be used as food, some for you, and the rest for them.”
Za ka ɗauki kowane irin abinci wanda za a ci, ka adana don yă zama abincinka da nasu.”
22 And so Noah did all things just as God had instructed him.
Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.

< Genesis 6 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water