< Genesis 47 >

1 And so Joseph entered and reported to Pharaoh, saying: “My father and brothers, their sheep and herds, and everything that they possess, have arrived from the land of Canaan. And behold, they stand together in the land of Goshen.”
Yusuf ya tafi yă faɗa wa Fir’auna, “Mahaifina da’yan’uwana, tare da garkunansu da shanunsu da kome da suke da shi, sun zo daga ƙasar Kan’ana, suna kuwa a Goshen yanzu.”
2 Likewise, he stood in the sight of the king five men, the last of his brothers.
Sai ya zaɓi mutum biyar daga cikin’yan’uwansa, ya gabatar da su a gaban Fir’auna.
3 And he questioned them, “What do you have for work?” They responded: “Your servants are pastors of sheep, both we and our fathers.
Fir’auna ya tambayi’yan’uwan, “Mece ce sana’arku?” Suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Bayinka makiyaya ne, kamar yadda kakanninmu suke.”
4 We came to sojourn in your land, because there is no grass for the flocks of your servants, the famine being very grievous in the land of Canaan. And we petition you that you may order us, your servants, to be in the land of Goshen.”
Suka kuma ce masa, “Mun zo, mu zauna a nan na ɗan lokaci, gama yunwa ta yi tsanani a Kan’ana, dabbobin bayinka kuma ba su da wurin kiwo. Saboda haka yanzu, muna roƙonka, bari bayinka su zauna a Goshen.”
5 And so the king said to Joseph: “Your father and brothers have come to you.
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Mahaifinka da’yan’uwanka sun zo maka,
6 The land of Egypt is in your sight. Cause them to live in the best place, and deliver to them the land of Goshen. And if you know there to be industrious men among them, appoint these as foremen over my cattle.”
ƙasar Masar kuma tana gabanka, ka zaunar da mahaifinka da’yan’uwanka a sashe mafi kyau na ƙasar, bari su zauna a Goshen. Idan kuma ka ga waɗansu a cikinsu da suka fi dacewa, sai ka sa su lura mini da shanuna.”
7 After this, Joseph brought in his father to the king, and he stood him in his sight. He blessed him,
Sa’an nan Yusuf ya shigar da Yaƙub mahaifinsa, ya gabatar da shi a gaban Fir’auna. Bayan Yaƙub ya albarkaci Fir’auna,
8 and he questioned him: “How many are the days of the years of your life?”
sai Fir’auna ya tambaye shi, “Shekarunka nawa da haihuwa?”
9 He responded, “The days of my sojourn are one hundred and thirty years, few and unworthy, and they do not reach even to the days of the sojourning of my fathers.”
Yaƙub kuwa ya ce wa Fir’auna, “Shekarun hijirata, shekaru ɗari da talatin ne. Shekaruna kaɗan ne cike da wahala, ba za a kuwa daidaita su da shekarun hijirar kakannina ba.”
10 And blessing the king, he went outside.
Sai Yaƙub ya albarkaci Fir’auna, ya yi masa bankwana, sa’an nan ya fita.
11 Truly, Joseph gave his father and brothers a possession in Egypt, in the best place of the land, in Rameses, as Pharaoh had instructed.
Ta haka Yusuf ya zaunar da mahaifinsa da’yan’uwansa a Masar, ya ba su mallaka a sashe mafi kyau na ƙasar, a yankin nan na Rameses, kamar yadda Fir’auna ya umarta.
12 And he fed them, along with all his father’s house, providing portions of food to each one.
Yusuf ya kuma tanada wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa da dukan gidan mahaifinsa, abinci bisa ga yawan’ya’yansu.
13 For in the whole world there was a lack of bread, and a famine had oppressed the land, most of all Egypt and Canaan,
A yanzu, a cikin ƙasar duka, ba abinci, gama yunwa ta yi tsanani ƙwarai, har ƙasar Masar da ƙasar Kan’ana suka shiga matsananciyar wahala!
14 from which he gathered together all the money for the grain that they bought, and he took it into the treasury of the king.
Yusuf ya tattara dukan kuɗaɗen da suke a Masar da Kan’ana don biyan hatsin da suke saya, ya kuwa kawo su a fadan Fir’auna.
15 And when the buyers had run out of money, all Egypt came to Joseph, saying: “Give us bread. Why should we die in your sight, lacking money?”
Sa’ad da kuɗin mutanen Masar da Kan’ana suka ƙare, dukan Masar ta zo wurin Yusuf ta ce, “Ka ba mu abinci. Me zai sa mu mutu a idanunka? Kuɗinmu duk sun ƙare.”
16 And he responded to them: “Bring me your cattle, and I will give food to you in exchange for them, if you do not have money.”
Yusuf ya ce, “To, ku kawo dabbobinku, zan sayar muku da abinci a madadin dabbobinku, tun da kuɗinku ya ƙare.”
17 And when they had brought them, he gave them food for their horses, and sheep, and oxen, and donkeys. And he sustained them in that year in exchange for their cattle.
Saboda haka suka kawo dabbobinsu wa Yusuf, ya kuma ba su abinci a madadin dawakai, tumaki da awaki, shanu da jakunansu. Ya kuwa ba su abinci a madadin dabbobinsu, a wannan shekara.
18 Likewise, they came the second year, and they said to him: “We will not conceal from our lord that our money is gone; likewise our cattle are gone. Neither are you unaware that we have nothing left but our bodies and our land.
Sa’ad da wannan shekara ta ƙare, sai suka zo wurinsa a shekara ta biye suka ce, “Ba za mu ɓoye maka ba ranka yă daɗe, kuɗinmu sun ƙare, dabbobinmu kuma sun zama naka. Ranka yă daɗe, in ban da jikunanmu da gonakinmu, ba abin da ya rage mana.
19 Therefore, why should you watch us die? Both we and our land will be yours. Buy us into royal servitude, but provide seed, lest by the dying off of cultivators the land be reduced to a wilderness.”
Kada ka bar mu mu mutu, ka yi wata dabara! Kada ka bari mu rasa gonakinmu. Ka musaye mu da abinci, mu da gonakinmu. Mu kuwa za mu zama bayin Fir’auna. Ka ba mu iri don mu rayu, kada mu mutu, don kuma kada gonakin ƙasarmu su zama kango.”
20 Therefore, Joseph bought all the land of Egypt, each one selling his possessions because of the magnitude of the famine. And he subjected it to Pharaoh,
Ta haka Yusuf ya saya wa Fir’auna ƙasar Masar duka, gama Masarawa duka sun sayar da gonakinsu, saboda yunwa ta tsananta musu. Ƙasar ta zama mallakar Fir’auna.
21 along with all of its people, from the newest borders of Egypt, even to its furthest limits,
Yusuf kuwa ya mai da mutanen bayi, daga wannan iyakar Masar zuwa wancan.
22 except the land of the priests, which had been delivered to them by the king. To these also a portion of food was supplied out of the public storehouses, and, for this reason, they were not compelled to sell their possessions.
Amma bai sayi gonakin firistoci ba, gama suna karɓa rabo daga Fir’auna ne, suna kuma da isashen abinci daga rabon da Fir’auna yake ba su. Dalilin ke nan da ba su sayar da gonakinsu ba.
23 Therefore, Joseph said to the people: “So, as you discern, both you and your lands are possessed by Pharaoh; take seed and sow the fields,
Yusuf ya ce wa mutane, “Yanzu da na saye ku da kuma gonakinku a yau wa Fir’auna, ga iri don ku shuka a gonaki.
24 so that you may be able to have grain. One fifth part you will give to the king; the remaining four I permit to you, as seed and as food for your families and children.
Amma sa’ad da hatsi suka nuna, za ku ba da kashi ɗaya bisa biyar ga Fir’auna. Sauran kashi huɗu bisa biyar kuma ku riƙe a matsayin iri don gonaki da kuma abinci wa kanku da gidajenku da kuma’ya’yanku.”
25 And they responded: “Our health is in your hand; only let our lord look kindly upon us, and we will serve the king with gladness.”
Suka ce, “Ka ceci rayukanmu, in ya gamshe ka, ranka yă daɗe, za mu zama bayin Fir’auna.”
26 From that time, even to the present day, in the entire land of Egypt, the fifth part is turned over to the kings, and it has become like a law, except in the land of the priests, which was free from this condition.
Ta haka Yusuf ya kafa wannan ya zama doka game da ƙasa a Masar, har yă zuwa yau cewa kashi ɗaya bisa biyar na amfani gona ya zama na Fir’auna. Gonakin firistoci ne kaɗai ba su zama na Fir’auna ba.
27 And so, Israel lived in Egypt, that is, in the land of Goshen, and he possessed it. And he increased and was multiplied exceedingly.
To, Isra’ilawa suka zauna a Masar a yankin Goshen. Suka mallaki filaye a can, suka riɓaɓɓanya suka ƙaru ƙwarai.
28 And he lived in it seventeen years. And all the days of his life that passed were one hundred and forty-seven years.
Yaƙub ya yi zama a Masar shekaru goma sha bakwai, yawan shekarunsa duka sun zama ɗari da arba’in da bakwai.
29 And when he discerned that the day of his death was approaching, he called his son Joseph, and he said to him: “If I have found favor in your sight, place your hand under my thigh. And you shall show me mercy and truth, not to bury me in Egypt.
Sa’ad da lokaci ya gabato da Isra’ila zai mutu, sai ya kira ɗansa Yusuf, ya ce masa, “Ka yi mini wannan alheri, ka sa hannunka ƙarƙashin cinyar ƙafata, ka yi mini alkawari saboda ina roƙonka kaɗa ka bizne ni a Masar,
30 But I shall sleep with my fathers, and you will carry me from this land and bury me in the sepulcher of my ancestors.” And Joseph answered him, “I will do what you have ordered.”
amma sa’ad da na huta da kakannina, ka ɗauke ni, ka fid da ni daga Masar, ka binne ni a inda aka binne su.” Yusuf ya ce, “Zan yi yadda ka faɗa.”
31 And he said, “Then swear it to me.” And as he was swearing, Israel adored God, turning to the head of his resting place.
Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini.” Sai Yusuf ya rantse masa, Isra’ila kuwa ya yi godiya ga Allah yayinda ya jingina a kan sandansa.

< Genesis 47 >