< Genesis 45 >

1 Joseph was unable to restrain himself any longer, standing before so many. Therefore, he instructed that all should go outside, and that no stranger should be among them as they recognized one another.
Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
2 And he lifted up his voice with weeping, which the Egyptians heard, along with the entire house of Pharaoh.
Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
3 And he said to his brothers: “I am Joseph. Is my father still alive?” His brothers were unable to respond, being terrified by a very great fear.
Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
4 And he said to them mildly, “Approach toward me.” And when they had approached close by, he said: “I am Joseph, your brother, whom you sold into Egypt.
Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
5 Do not be afraid, and let it not seem to you to be a hardship that you sold me into these regions. For God sent me before you into Egypt for your salvation.
Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
6 For it is two years since the famine began to be upon the land, and five years more remain, in which there can be neither plowing, nor reaping.
Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
7 And God sent me ahead, so that you may be preserved upon the earth, and so that you would be able to have food in order to live.
Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
8 I was sent here, not by your counsel, but by the will of God. He has caused me to be like a father to Pharaoh, and to be the lord of his entire house, as well as governor throughout all the land of Egypt.
“Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
9 Hurry, and go up to my father, and say to him: ‘Your son Joseph commands this: God has caused me to be lord of the entire land of Egypt. Come down to me, do not delay,
Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
10 and you will live in the land of Goshen. And you will be next to me, you and your sons and the sons of your sons, your sheep and your herds, and all that you possess.
Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
11 And there I will pasture you, (for there are still five years of famine remaining) lest both you and your house perish, along with all that you possess.’
Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
12 Behold, your eyes and the eyes of my brother Benjamin can see that it is my mouth speaking to you.
“Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
13 You will report to my father about all my glory, and about all that you have seen in Egypt. Hurry, and bring him to me.”
Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
14 And then falling upon the neck of his brother Benjamin, he embraced him and wept. And likewise, Benjamin wept at the same time on his neck.
Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
15 And Joseph kissed all his brothers, and he cried over each one. After this, they were emboldened to speak to him.
Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
16 And it was overheard, and the news spread by word throughout the king’s court. The brothers of Joseph had arrived, and Pharaoh was gladdened along with all his family.
Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
17 And he told Joseph that he should command his brothers, saying: “‘Burden your beasts, and go into the land of Canaan,
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
18 and take from there your father and kindred, and come to me. And I will give you all the good things of Egypt, so that you may eat from the marrow of the land.’”
Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
19 “And you may even instruct that they take wagons from the land of Egypt, in order to transport their little ones as well as their wives. And say: ‘Take your father, and come quickly, as soon as possible.
“An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
20 You need not give up anything from your household, for all the riches of Egypt will be yours.’”
Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
21 And the sons of Israel did just as they were commanded. And Joseph gave them wagons, according to the command of Pharaoh, and provisions for the journey.
Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
22 Likewise, he ordered two robes for each of them to be brought. Yet truly, to Benjamin he gave three hundred pieces of silver along with five of the best robes.
Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
23 And he sent just as much money and clothing to his father, adding also ten male donkeys, with which to transport all the riches of Egypt, and as many female donkeys, carrying wheat and bread for the journey.
Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
24 Thus he sent away his brothers, and as they set out he said, “Do not become angry on the way.”
Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
25 And they ascended out of Egypt, and they arrived in the land of Canaan, to their father Jacob.
Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
26 And they reported to him, saying: “Your son Joseph is alive, and he is ruler throughout all the land of Egypt. When Jacob heard this, he was stirred up, as if from a deep sleep, yet he did not believe them.
Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
27 To the contrary, they explained the entire matter in order. And when he had seen the wagons, and all that he had sent, his spirit revived,
Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
28 and he said: “It is enough for me, if my son Joseph is still alive. I will go and see him before I die.”
Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”

< Genesis 45 >