< Genesis 43 >

1 Meanwhile, the famine pressed heavily on all the land.
A yanzu, yunwa ta yi tsanani a ƙasar.
2 And having consumed the provisions that they had brought out of Egypt, Jacob said to his sons, “Return and buy us a little food.”
Saboda haka sa’ad da suka cinye dukan hatsin da suka kawo daga Masar, mahaifinsu ya ce musu, “Ku koma, ku sayo mana ƙarin abinci.”
3 Judah answered: “The man himself declared to us, under the attestation of an oath, saying: ‘You will not see my face, unless you bring your youngest brother with you.’
Amma Yahuda ya ce masa, “Mutumin ya gargaɗe mu sosai cewa, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai in ɗan’uwanku yana tare da ku.’
4 If therefore you are willing to send him with us, we will travel together, and we will buy necessities for you.
In za ka aika da ɗan’uwanmu tare da mu, za mu gangara mu sayo maka abinci.
5 But if you are not willing, we will not go. For the man, as we have often said, declared to us, saying: ‘You will not see my face without your youngest brother.’”
Amma in ba za ka aika da shi ba, ba za mu gangara ba, gama mutumin ya ce mana, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai ko in ɗan’uwanku yana tare da ku.’”
6 Israel said to them, “You have done this for my misery, in that you revealed to him that you also had another brother.”
Isra’ila ya yi tambaya, “Me ya sa kuka kawo wannan damuwa a kaina ta wurin faɗa wa mutumin cewa kuna da wani ɗan’uwa?”
7 But they responded: “The man questioned us in order, concerning our family: whether our father lived, if we had a brother. And we answered him respectively, according to what he demanded. How could we know that he would say, ‘Bring your brother with you?’”
Suka amsa, “Mutumin ya yi mana tambaya sosai game da kanmu da iyalinmu. Ya tambaye mu, ‘Mahaifinku yana da rai har yanzu? Kuna da wani ɗan’uwa?’ Mu dai mun amsa tambayoyinsa ne. Ta yaya za mu sani zai ce, ‘Ku kawo ɗan’uwanku a nan’?”
8 Likewise, Judah said to his father: “Send the boy with me, so that we may set out and be able to live, lest we and our little ones should die.
Sa’an nan Yahuda ya ce wa Isra’ila mahaifinsa, “Ka aika saurayin tare da ni za mu kuwa tafi nan da nan, saboda mu da’ya’yanmu mu rayu, kada mu mutu.
9 I accept the boy; require him at my hand. Unless I lead him back and restore him to you, I will be guilty of a sin against you for all time.
Ni kaina zan tabbatar da lafiyarsa; na ɗauki lamuninsa, a hannuna za ka neme shi. In ban dawo da shi gare ka, in sa shi nan a gabanka ba, zan ɗauki laifin a gabanka dukan kwanakina.
10 If a delay had not intervened, by now we would have returned here a second time.”
Ai, da ba mun jinkirta ba, da mun komo har sau biyu.”
11 Therefore, their father Israel said to them: “If it is necessary to do so, then do what you will. Take, in your vessels, from the best fruits of the land, and carry down gifts to the man: a little resin, and honey, and storax ointment, oil of myrrh, turpentine, and almonds.
Sa’an nan mahaifinsu Isra’ila ya ce musu, “In dole ne a yi haka, to, sai ku yi. Ku sa waɗansu amfani mafi kyau na ƙasar a buhunanku, ku ɗauka zuwa wurin mutumin a matsayin kyauta, da ɗan man ƙanshi na shafawa, da kuma’yar zuma, da kayan yaji, da ƙaro, da tsabar citta da kuma almon.
12 Also, take with you double the money, and carry back what you found in your sacks, lest perhaps it was done in error.
Ku ɗauki ninki biyu na yawan azurfa tare da ku, gama dole ku mayar da azurfan da aka sa a cikin bakunan buhunanku. Mai yiwuwa an yi haka a kuskure ne.
13 But also take your brother, and go to the man.
Ku ɗauki ɗan’uwanku kuma ku koma wurin mutumin nan da nan.
14 Then may my Almighty God cause him to be pleased by you. And send your brother, whom he holds, back with you, along with this one, Benjamin. But as for me, without my children, I will be like one who is bereaved.”
Bari Allah Maɗaukaki yă nuna muku alheri a gaban mutumin saboda yă bar ɗan’uwanku da Benyamin su dawo tare da ku. Ni kuwa, in na yi rashi, na yi rashi.”
15 Therefore, the men took the gifts, and double the money, and Benjamin. And they went down into Egypt, and they stood in the presence of Joseph.
Saboda haka mutanen suka ɗauki kyautar, da kuma kuɗin da ya ninka na farko. Suka kuma ɗauki Benyamin, suka gaggauta suka gangara zuwa Masar suka kuma gabatar da kansu ga Yusuf.
16 And when he had seen them and Benjamin together, he instructed the steward of his house, saying: “Lead the men into the house, and kill victims, and prepare a feast, because they will be eating with me at midday.”
Sa’ad da Yusuf ya ga Benyamin tare da su, sai ya ce wa mai hidimar gidansa, “Ka shigar da mutanen cikin gida, ka yanka dabba ka shirya, gama mutanen za su ci abincin rana tare da ni.”
17 He did what he had been ordered to do, and he brought the men into the house.
Mutumin ya yi kamar yadda Yusuf ya faɗa masa, ya kuwa ɗauki mutanen zuwa gidan Yusuf.
18 And there, being terrified, they said one to another: “Because of the money, which we carried back the first time in our sacks, we have been brought in, so that he may unleash a false accusation against us, and by violence subjugate both us and our donkeys into servitude.”
Mutanen dai suka firgita sa’ad da aka ɗauke su zuwa gidansa. Suka yi tunani, “An kawo mu nan ne saboda azurfan da aka sa a cikin buhunanmu da farko. Yana so yă fāɗa mana, yă kuma sha ƙarfinmu, yă ƙwace mu kamar bayi, yă kuma kwashe jakunanmu.”
19 For this reason, approaching the steward of the house at his door,
Saboda haka suka je wurin mai yin wa Yusuf hidima, suka yi masa magana a bakin ƙofar gida.
20 they said: “We beg you, lord, to hear us. We came down once before to buy food.
Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun zo nan ƙaro na farko don mu saya abinci,
21 And having bought it, when we arrived at the inn, we opened our sacks and found the money in the mouths of the sacks, which we now have carried back in the same amount.
amma a inda muka tsaya don mu kwana, da muka buɗe buhunanmu sai kowannenmu ya sami azurfansa daidai a bakin buhunsa. Saboda haka ga kuɗin a hannunmu, mun sāke komowa da su.
22 But we have also brought other silver, so that we may buy those things that are necessary for us. It is not on our conscience who had placed it in our bags.”
Mun kuma kawo ƙarin azurfa tare da mu don mu saya abinci. Ba mu san wa ya sa azurfanmu a cikin buhunanmu ba.”
23 But he responded: “Peace be with you. Do not be afraid. Your God, and the God of your father, has given you the treasure in your sacks. As for the money that you gave to me, I held it as a test.” And he led Simeon out to them.
Sai mai hidimar ya ce, “Ba kome, kada ku ji tsoro. Allahnku, Allahn mahaifinku ne ya ba ku dukiyar a cikin buhunanku; ni dai, na karɓi azurfanku.” Sa’an nan ya fitar musu da Simeyon.
24 And having led them into the house, he brought water, and they washed their feet, and he gave fodder to their donkeys.
Mai yin hidimar ya ɗauki mutane zuwa gidan Yusuf ya ba su ruwa su wanke ƙafafunsu, ya kuma tanada wa jakunansu abinci.
25 But they also prepared the gifts, until Joseph entered at midday. For they had heard that they would eat bread there.
Suka shirya kyautansu domin isowar Yusuf da rana, gama sun ji cewa zai ci abinci a nan.
26 And so Joseph entered his house, and they offered him the gifts, holding them in their hands. And they reverenced prone on the ground.
Sa’ad da Yusuf ya zo gida, sai suka ba shi kyautai da suka kawo, suka rusuna a gabansa har ƙasa.
27 But he, gently greeting them again, questioned them, saying: “Is your father, the old man about whom you spoke to me, in good health? Is he still alive?”
Ya tambaye su, yaya suke, sa’an nan ya ce, “Yaya tsohon nan mahaifinku da kuka faɗa mini? Yana da rai har yanzu?”
28 And they answered: “Your servant, our father, is safe; he is still alive.” And bowing, they reverenced him.
Suka amsa, “Bawanka mahaifinmu yana da rai har yanzu da kuma ƙoshin lafiya.” Suka kuma rusuna suka yi mubaya’a.
29 Then Joseph, lifting up his eyes, saw Benjamin, his brother of the same womb, and he said, “Is this your little brother, about whom you spoke to me?” And again, he said, “May God be compassionate to you, my son.”
Da ya ɗaga idanu, sai ya ga ɗan’uwansa Benyamin, ɗan mahaifiyarsa, sai ya yi tambaya, “Wannan ne ƙaramin ɗan’uwanku, wanda kuka faɗa mini a kai?” Ya kuma ce, “Allah yă yi maka albarka, ɗana.”
30 And he hurried out, because his heart had been moved over his brother, and tears gushed out. And going into his chamber, he wept.
Saboda motsi mai zurfi da zuciyarsa ta yi da ganin ɗan’uwansa, sai Yusuf ya gaggauta ya fita, ya nemi wuri yă yi kuka. Ya shiga ɗakinsa ya yi kuka a can.
31 And when he had washed his face, coming out again, he composed himself, and he said, “Set out bread.”
Bayan ya wanke fuskarsa, sai ya fito ya daure, ya umarta, “A kawo abinci.”
32 And when it was set out, separately for Joseph, and separately for his brothers, likewise separately for the Egyptians, who ate at the same time, (for it is unlawful for Egyptians to eat with Hebrews, and they consider feasting in this way to be profane)
Sai aka raba musu abinci, nasa shi kaɗai su kuma su kaɗai, domin Masarawa ba sa cin abinci tare da Ibraniyawa, gama wannan abin ƙyama ne ga Masarawa.
33 they sat before him, the firstborn according to his birthright, and the youngest according to his state of life. And they wondered exceedingly,
Aka zaunar da’yan’uwan Yusuf a gabansa bisa ga shekarunsu, daga ɗan fari zuwa auta.’Yan’uwan kuwa suka duddubi juna suna mamaki.
34 taking the portions that they received from him. And the greater portion went to Benjamin, so much so that it exceeded five parts. And they drank and became inebriated along with him.
Daga teburin da yake a gaban Yusuf aka riƙa ɗibar rabonsu ana kai musu, amma rabon Benyamin ya yi biyar ɗin na kowannensu. Suka kuwa sha, suka yi murna tare da shi.

< Genesis 43 >