< Genesis 42 >

1 Then Jacob, hearing that food was being sold in Egypt, said to his sons: “Why are you negligent?
Sa’ad da Yaƙub ya sami labari cewa akwai hatsi a Masar, sai ya ce wa’ya’yansa maza, “Don me kuke duban juna kawai?”
2 I have heard that wheat is being sold in Egypt. Go down and buy necessities for us, so that we may be able to live, and not be consumed by destitution.”
Ya ci gaba, “Na ji cewa akwai hatsi a Masar. Ku gangara can ku sayo mana, domin mu rayu kada mu mutu.”
3 And so, when ten brothers of Joseph went down to buy grain in Egypt,
Sai goma daga cikin’yan’uwan Yusuf suka gangara don su saya hatsi daga Masar.
4 Benjamin was kept at home by Jacob, who said to his brothers, “Lest perhaps he may suffer harm on the journey.”
Amma Yaƙub bai aiki Benyamin, ɗan’uwan Yusuf tare da sauran ba, gama yana tsoro kada wani abu yă faru da shi.
5 And they entered into the land of Egypt with the others who traveled to buy. For the famine was in the land of Canaan.
Sai’ya’yan Yaƙub suka isa Masar tare da sauran mutanen don sayen abinci, gama yunwar ta kai yankin Kan’ana ma.
6 And Joseph was governor in the land of Egypt, and grain was sold under his direction to the people. And when his brothers had reverenced him
To, Yusuf ne gwamnar ƙasar wanda yake sayar da hatsi ga dukan mutanenta. Saboda haka sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka isa, sai suka rusuna masa har ƙasa da fuskokinsu.
7 and he had recognized them, he spoke harshly, as if to foreigners, questioning them: “Where did you come from?” And they responded, “From the land of Canaan, to buy necessary provisions.”
Nan da nan da Yusuf ya ga’yan’uwansa, sai ya gane su, amma ya yi kamar baƙo, ya kuma yi musu magana da tsawa. Ya tambaya, “Daga ina kuka fito?” Suka amsa, “Daga ƙasar Kan’ana, don mu saya abinci.”
8 And although he knew his brothers, he was not known by them.
Ko da yake Yusuf ya gane’yan’uwansa, su ba su gane shi ba.
9 And remembering the dreams, which he had seen in another time, he said to them: “You are scouts. You have come in order to see which parts of the land are weaker.”
Sa’an nan ya tuna da mafarkansa game da su, ya kuma ce musu, “Ku’yan leƙen asiri ne! Kun zo don ku leƙi asirin ƙasar ku ga inda ba ta da tsaro.”
10 And they said: “It is not so, my lord. But your servants have arrived in order to buy food.
Suka amsa suka ce, “A’a, ranka yă daɗe, bayinka sun zo don saya abinci ne.
11 We are all sons of one man. We have come in peace, nor do any of your subjects devise evil.”
Mu duka’ya’yan mutum ɗaya maza ne. Bayinka mutane ne masu gaskiya, ba’yan leƙen asiri ba ne.”
12 And he answered them: “It is otherwise. You have come to examine the unguarded parts of this land.”
Ya ce musu “Sam! Kun zo ne ku ga inda ƙasarmu babu tsaro.”
13 But they said: “We, your servants, are twelve brothers, the sons of one man in the land of Canaan. The youngest is with our father; the other is not living.”
Amma suka amsa suka ce, “Bayinka dā su goma sha biyu ne,’yan’uwa,’ya’yan mutum guda maza, wanda yake zama a ƙasar Kan’ana. Ƙaraminmu yanzu yana tare da mahaifinmu, ɗayan kuma ya rasu.”
14 He said: “This is just as I have said. You are scouts.
Yusuf ya ce musu, “Daidai ne yadda na faɗa muku. Ku’yan leƙen asiri ne!
15 I will now continue to put you to the test. By the health of Pharaoh, you will not depart from here, until your youngest brother arrives.
Ga kuwa yadda za a gwada ku. Muddin Fir’auna yana a raye, ba za ku bar wannan wuri ba sai ƙaramin ɗan’uwanku ya zo nan.
16 Send one of you and bring him. But you will be in chains, until what you have said is proven to be either true or false. Otherwise, by the health of Pharaoh, you are scouts.”
Ku aiki ɗaya daga cikinku yă kawo ɗan’uwanku; za a sa sauranku a kurkuku, saboda a gwada maganarku a ga ko gaskiya ce kuke faɗi. In ba haka ba, to, da ran Fir’auna, ku’yan leƙen asiri ne!”
17 Therefore, he delivered them into custody for three days.
Ya kuwa sa su duka a kurkuku na kwana uku.
18 Then, on the third day, he brought them out of prison, and he said: “Do as I have said, and you will live. For I fear God.
A rana ta uku, Yusuf ya ce musu, “Ku yi wannan za ku kuwa rayu, gama ina tsoron Allah.
19 If you are peaceful, let one of your brothers be bound in prison. Then you may go away and carry the grain that you have bought to your houses.
In ku mutane masu gaskiya ne, ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku yă zauna a kurkuku, yayinda sauranku su tafi, su kai hatsi don gidajenku da suke yunwa.
20 And bring your youngest brother to me, so that I may be able to test your words, and you may not die.” They did as he had said,
Amma dole ku kawo ƙaramin ɗan’uwanku gare ni, saboda a tabbatar da maganarku har ba za ku mutu ba.” Suka kuwa yi haka.
21 and they spoke to one another: “We deserve to suffer these things, because we have sinned against our brother, seeing the anguish of his soul, when he begged us and we would not listen. For that reason, this tribulation has come upon us.”
Sai suka ce wa juna, “Tabbatacce ana hukunta mu ne saboda ɗan’uwanmu. Mun ga yadda ya yi wahala sa’ad da ya roƙe mu saboda ransa, amma ba mu saurare shi ba, shi ya sa wannan wahala ta zo mana.”
22 And Reuben, one of them, said: “Did not I say to you, ‘Do not sin against the boy,’ and you would not listen to me? See, his blood is exacted.”
Ruben ya amsa, “Ban faɗa muku cewa kada ku ɗauki alhakin yaron nan ba, sai kuka ƙi ji, to, yau ga alhakin jininsa muke biya.”
23 But they did not know that Joseph understood, because he was speaking to them through an interpreter.
Ba su san cewa Yusuf yana jin su ba, da yake yana amfani da mai fassara ne.
24 And he turned himself away briefly and wept. And returning, he spoke to them.
Sai ya juya daga gare su ya yi kuka, sa’an nan ya dawo ya yi musu magana kuma. Ya sa aka ɗauke Simeyon daga gare su, aka daure shi a idanunsu.
25 And taking Simeon, and binding him in their presence, he ordered his ministers to fill their sacks with wheat, and to replace each one’s money in their sacks, and to give them, in addition, provisions for the way. And they did so.
Yusuf ya yi umarni a cika buhunansu da hatsi, a kuma sa azurfan kowane mutum a cikin buhunsa, a kuma ba su kalaci don tafiyarsu. Bayan aka yi musu wannan,
26 Then, having loaded their donkeys with the grain, they set out.
suka jibga hatsinsu a kan jakuna, sai suka kama hanya.
27 And one of them, opening a sack to give his beast of burden fodder at the inn, looked upon the money at the sack’s mouth,
A wurin da suka tsaya don su kwana, ɗaya daga cikinsu ya buɗe buhunsa don yă ciyar da jakinsa, sai ya ga azurfansa a bakin buhunsa.
28 and he said to his brothers: “My money has returned to me. See, it is held in the sack.” And they were astonished and troubled, and they said to one another, “What is this that God has done to us?”
Sai ya ce wa’yan’uwansa, “An mayar mini da azurfata. Ga shi a cikin buhuna.” Zuciyarsu ta karai, suka dubi juna suna rawan jiki, suka ce, “Mene ne wannan da Allah ya yi mana?”
29 And they went to their father Jacob in the land of Canaan, and they explained to him all the things that had befallen them, saying:
Sa’ad da suka zo wurin mahaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana, suka faɗa masa dukan abin da ya faru da su. Suka ce,
30 “The lord of the land spoke harshly to us, and he considered us to be scouts of the province.
“Mutumin da yake shugaba a ƙasar ya yi mana matsananciyar magana, ya kuma ɗauke mu tamƙar’yan leƙen asirin ƙasa.
31 And we answered him: ‘We are peaceful, and we do not intend any treachery.
Amma muka ce masa, ‘Mu masu gaskiya ne; mu ba’yan leƙen asiri ba ne.
32 We are twelve brothers conceived of one father. One is not living; the youngest is with our father in the land of Canaan.’
Dā mu’yan’uwa ne goma sha biyu,’ya’yan mahaifi guda maza. Ɗayanmu ya rasu, kuma ƙaramin yanzu yana tare da mahaifinmu a Kan’ana.’
33 And he said to us: ‘Thus will I prove that you are peaceful. Release one of your brothers to me, and take necessary provisions for your houses, and go away,
“Sai mutumin wanda yake shugaba a kan ƙasar ya ce mana, ‘Ga yadda zan san ko ku mutane masu gaskiya ne. Ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku a nan tare da ni, ku ɗauki abinci domin gidajenku masu yunwa, ku tafi.
34 and bring your youngest brother to me, so that I may know that you are not scouts. And this one, who is held in chains, you may be able to receive again. And thereafter, you shall have permission to buy what you want.’”
Amma ku kawo mini ƙaramin ɗan’uwanku domin in san cewa ku ba’yan leƙen asiri ba ne, amma mutane ne masu gaskiya. Sa’an nan zan mayar muku da ɗan’uwanku, ku kuma iya yin sana’a a ƙasar.’”
35 Having said this, when they poured out their grain, each found his money tied to the mouth of his sack. And all were terrified together.
Yayinda suke juyewa hatsi daga buhunansu, sai ga ƙunshin azurfan kowane mutum a buhunsa! Sa’ad da su da mahaifinsu suka ga ƙunshe-ƙunshen kuɗi, suka firgita.
36 Their father Jacob said, “You have caused me to be without children. Joseph is not living, Simeon is held in chains, and Benjamin you would carry away. All these evils have fallen back upon me.”
Yaƙub mahaifinsu, ya ce musu, “Kun sa ni rashin’ya’yana. Yusuf ya rasu, Simeyon kuma ba ya nan, yanzu kuma kuna so ku ɗauki Benyamin. Kome yana gāba da ni!”
37 And Reuben answered him, “Put my two sons to death, if I do not lead him back to you. Deliver him into my hand, and I will restore him to you.”
Sai Ruben ya ce wa mahaifinsa, “Ka kashe dukan’ya’yana maza, in ban dawo da shi gare ka ba. Ka sa shi ga kulawata, zan kuwa dawo da shi.”
38 But he said: “My son will not go down with you. His brother is dead, and he is left alone. If any adversity will befall him in the land to which you travel, you would lead my grey hairs down with sorrow to the grave.” (Sheol h7585)
Amma Yaƙub ya ce, “Ɗana ba zai gangara zuwa can tare da ku ba, ɗan’uwansa ya rasu, shi ne kaɗai ya rage. In wani abu ya faru da shi a tafiyar da za ku yi, za ku sa furfurata ta gangara zuwa kabari cikin baƙin ciki.” (Sheol h7585)

< Genesis 42 >