< Genesis 38 >

1 About the same time, Judah, descending from his brothers, turned toward an Adullamite man, named Hirah.
A wannan lokaci, Yahuda ya bar’yan’uwansa ya gangara don yă zauna da mutumin Adullam, mai suna Hira.
2 And he saw there the daughter of a man called Shua, of Canaan. And taking her as a wife, he entered to her.
A can Yahuda ya sadu da’yar wani Bakan’ane, mai suna Shuwa. Ya aure ta, ya kuma kwana da ita;
3 And she conceived and bore a son, and she called his name Er.
ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa, wanda aka kira Er.
4 And conceiving offspring again, having given birth to a son, she called him Onan.
Ta sāke yin ciki, ta haifi wani ɗa, ta kira shi Onan.
5 Likewise, she bore a third, whom she called Shelah, after whose birth, she ceased to bear any more.
Ta kuma haifi wani ɗa har yanzu, aka kuwa ba shi suna Shela. A Kezib ne ta haife shi.
6 Then Judah gave a wife to his first born Er, whose name was Tamar.
Sai Yahuda ya auro wa Er mata, ɗansa na fari, sunanta Tamar.
7 And it also happened that Er, the first born of Judah, was wicked in the sight of the Lord and was killed by him.
Amma Er, ɗan farin Yahuda mugu ne a fuskar Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi.
8 Therefore, Judah said to his son Onan: “Enter to the wife of your brother, and associate with her, so that you may raise offspring to your brother.”
Sa’an nan Yahuda ya ce wa Onan, “Ka kwana da matar ɗan’uwanka ka cika wajibinka gare ta a matsayin ɗan’uwan miji, don ka samar wa ɗan’uwanka’ya’ya.”
9 He, knowing that the sons to be born would not be his, when he entered to the wife of his brother, he spilled his seed on the ground, lest children should be born in his brother’s name.
Amma Onan ya san cewa’ya’yan ba za su zama nasa ba; saboda haka a duk sa’ad da ya kwana da matar ɗan’uwansa, sai yă zub da maniyyinsa a ƙasa don kada yă samar wa ɗan’uwansa’ya’ya.
10 And for this reason, the Lord struck him down, because he did a detestable thing.
Abin nan da ya yi mugunta ce a gaban Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi, shi ma.
11 Because of this matter, Judah said to his daughter-in-law Tamar, “Be a widow in your father’s house, until my son Shelah grows up.” For he was afraid, lest he also might die, just as his brothers did. She went away, and she lived in her father’s house.
Sai Yahuda ya ce wa surukarsa Tamar, “Ki yi zama kamar gwauruwa a gidan mahaifinki sai ɗana Shela ya yi girma.” Gama ya yi tunani, “Shi ma zai mutu, kamar’yan’uwansa.” Saboda haka Tamar ta je ta zauna a gidan mahaifinta.
12 Then, after many days had passed, the daughter of Shua, the wife of Judah, died. And when he accepted consolation after his mourning, he went up to the shearers of his sheep at Timnah, he and Hirah, the herdsman of the Adullamite flock.
Bayan an daɗe sai matar Yahuda,’yar Shuwa ta rasu. Sa’ad da Yahuda ya gama makoki, sai ya haura zuwa Timna, zuwa wurin mutanen da suke askin tumakinsa, abokinsa Hira mutumin Adullam kuwa ya tafi tare da shi.
13 And it was reported to Tamar that her father-in-law had gone up to Timnah to shear the sheep.
Sa’ad da aka faɗa wa Tamar cewa, “Surukinki yana kan hanyarsa zuwa Timna don askin tumakinsa,”
14 And storing away the garments of her widowhood, she took up a veil. And changing her clothing, she sat at the crossroad that leads to Timnah, because Shelah had grown up, and she had not received him as a husband.
sai ta tuɓe rigunan gwaurancinta ta rufe kanta da lulluɓi don ta ɓad da kamanninta, sa’an nan ta je ta zauna a ƙofar shigar Enayim, wadda take a hanyar zuwa Timna. Gama ta lura cewa ko da yake Shela yanzu ya yi girma, ba a ba da ita gare shi ta zama matarsa ba.
15 And when Judah saw her, he thought her to be a harlot. For she had covered her face, lest she be recognized.
Sa’ad da Yahuda ya gan ta, ya yi tsammani karuwa ce, gama ta lulluɓe fuskarta.
16 And entering to her, he said, “Permit me to join with you.” For he did not know her to be his daughter-in-law. And she responded, “What will you give to me, to enjoy me as a concubine?”
Bai san cewa ita surukarsa ce ba, sai ya ratse zuwa wurinta a gefen hanya ya ce, “Zo mana, in kwana da ke.” Sai ta ce, “Me za ka ba ni in na kwana da kai?”
17 He said, “I will send you a young goat from the flock.” And again, she said, “I will allow what you want, if you give me a pledge, until you may send what you promise.”
Ya ce, “Zan aika miki da ɗan akuya daga garkena.” Sai ta ce, “Za ka ba ni wani abu jingina, kafin ka aika da shi?”
18 Judah said, “What do you want to be given for a pledge?” She responded, “Your ring and bracelet, and the staff that you hold in your hand.” Thereupon, the woman, from one sexual encounter, conceived.
Ya ce, “Wace jingina zan ba ki?” Sai ta amsa, “Hatiminka da ka rataye a wuya da kuma sandan da yake a hannunka.” Ya ba da su gare ta, ya kuma kwana da ita, sai ta yi ciki.
19 And she arose and went away. And storing away the garments that she had taken up, she was clothed in the garments of her widowhood.
Bayan ta tafi, sai ta tuɓe lulluɓin, ta sāke sa tufafin gwaurancinta.
20 Then Judah sent a young goat by his shepherd, the Adullamite, so that he might receive the pledge that he had given to the woman. But, when he had not found her,
Ana cikin haka sai Yahuda ya aika da ɗan akuya ta hannun abokinsa mutumin Adullam don yă karɓo masa jinginar daga wurin macen, amma bai same ta a can ba.
21 he questioned the men of that place: “Where is the woman who sat at the crossroad?” And they all responded, “There has been no harlot in this place.”
Ya tambayi mutanen da suke zama a can ya ce, “Ina karuwar haikalin da take a bakin hanya a Enayim?” Sai suka ce, “Ba a taɓa kasance da karuwar haikali a nan ba.”
22 He returned to Judah, and he said to him: “I did not find her. Moreover, the men of that place told me that a prostitute had never sat there.”
Saboda haka sai ya koma zuwa wurin Yahuda ya ce, “Ban same ta ba. Ban da haka ma, mutanen da suke zama a can, sun ce, ‘Ba a taɓa kasance da wata karuwar haikali a nan ba.’”
23 Judah said: “Let her hold herself to blame. Certainly, she is not able to accuse us of a lie. I sent the young goat that I had promised, and you did not find her.”
Sa’an nan Yahuda ya ce, “Bari tă riƙe kayan kiɗa garin nema mu zama abin dariya. Ni kam, na aika da tunkiyar amma ba a same ta ba.”
24 And behold, after three months, they reported to Judah, saying, “Tamar, your daughter-in-law, has committed fornication and her abdomen appears to be enlarged.” And Judah said, “Produce her, so that she may be burned.”
Bayan misalin wata uku sai aka faɗa wa Yahuda cewa, “Tamar, surukarka ta yi laifin karuwanci, a sakamakon haka yanzu ta yi ciki.” Yahuda ya ce, “A fid da ita, a ƙone!”
25 But when she was led out to the punishment, she sent to her father-in-law, saying: “I conceived by the man to whom these things belong. Recognize whose ring, and bracelet, and staff this is.”
Yayinda ake fitar da ita, sai ta aika saƙo zuwa wurin surukinta, ta ce, “Mutumin da yake da waɗannan kayan ne ya yi mini ciki.” Ta kuma ƙara da cewa, “Duba ko za ka gane da hatimin nan, da abin ɗamaran nan, da kuma sandan nan, ko na wane ne?”
26 But he, acknowledging the gifts, said: “She is more just than I am. For I did not deliver her to my son Shelah.” However, he knew her no more.
Yahuda ya gane su, sai ya ce, “Ai, ta fi ni gaskiya, da yake ban ba da ita ga ɗana Shela ba.” Bai kuwa ƙara kwana da ita ba.
27 Then, at the moment of birth, there appeared twins in the womb. And so, in the very delivery of the infants, one put forth a hand, on which the midwife tied a scarlet thread, saying,
Sa’ad da lokaci ya yi da za tă haihu, ashe, tagwaye’yan maza ne suke cikinta.
28 “This one will go out first.”
Yayinda take haihuwa, ɗaya daga cikinsu ya fid da hannunsa; sai ungonzomar ta ɗauki jan zare ta ɗaura a hannun, ta ce, “Wannan ne ya fito da farko.”
29 But in truth, drawing back his hand, the other came out. And the woman said, “Why is the partition divided for you?” And for this reason, she called his name Perez.
Amma sa’ad da ya janye hannunsa, sai ɗan’uwansa ya fito, sai ta ce, “Wato, haka ne ka keta ka fito!” Sai aka ba shi suna Ferez.
30 After this, his brother came out, on whose hand was the scarlet thread. And she called him Zerah.
Sa’an nan ɗan’uwansa wanda yake da jan zare a hannunsa ya fito, aka kuma ba shi suna Zera.

< Genesis 38 >