< Genesis 37 >

1 Now Jacob lived in the land of Canaan, where his father sojourned.
Yaƙub ya zauna a ƙasar da mahaifinsa ya zauna, wato, ƙasar Kan’ana.
2 And these are his generations. Joseph, when he was sixteen years old, was pasturing the flock with his brothers, when he was still a boy. And he was with the sons of Bilhah and Zilpah, the wives of his father. And he accused his brothers to their father of a most sinful crime.
Wannan shi ne labarin zuriyar Yaƙub. Yusuf, saurayi ne mai shekara goma sha bakwai. Shi da’yan’uwansa, wato,’ya’yan Bilha maza da kuma’ya’yan Zilfa maza, matan mahaifinsa suna kiwon garkuna tare. Sai Yusuf ya kawo wa mahaifinsu rahoto marar kyau game da’yan’uwansa.
3 Now Israel loved Joseph above all his sons, because he had conceived him in his old age. And he made him a tunic, woven of many colors.
Isra’ila dai ya fi ƙaunar Yusuf fiye da kowanne a cikin sauran’ya’yansa maza, gama an haifa masa shi a cikin tsufansa. Sai ya yi masa riga mai gwanin kyau.
4 Then his brothers, seeing that he was loved by his father more than all his other sons, hated him, and they were not able to say anything peacefully to him.
Sa’ad da’yan’uwansa suka ga cewa mahaifinsu ya fi ƙaunarsa fiye da kowanne daga cikinsu, sai suka ƙi jininsa, ba sa kuma maganar alheri da shi.
5 Then it also happened that he recounted the vision of a dream to his brothers, for which reason a greater hatred began to be nurtured.
Sai Yusuf ya yi mafarki, sa’ad da ya faɗa wa’yan’uwansa, suka ƙara ƙin jininsa.
6 And he said to them, “Listen to my dream that I saw.
Ya ce musu, “Ku saurari wannan mafarkin da na yi.
7 I thought we were binding sheaves in the field. And my sheaf seemed to rise up and stand, and your sheaves, standing in a circle, reverenced my sheaf.”
Muna daurin dammunan hatsi a gona, sai nan da nan damina ya tashi ya tsaya, yayinda dammunanku suka taru kewaye da nawa suka rusuna masa.”
8 His brothers responded: “Would you be our king? Or will we be subject to your dominion?” Therefore, this matter of his dreams and words provided kindling to their envy and hatred.
Sai’yan’uwansa suka ce masa, “Kana nufin za ka yi mulki a kanmu ke nan? Ko kuwa za ka zama sarki, a bisanmu?” Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkinsa da kuma abin da ya faɗa.
9 Likewise, he saw another dream, which he explained to his brothers, saying, “I saw by a dream, as if the sun, and the moon, and eleven stars were reverencing me.”
Sai Yusuf ya sāke yin wani mafarki, ya faɗa wa’yan’uwansa. Ya ce, “Ku saurara, na sāke yin wani mafarki, a wannan lokaci, na ga rana da wata da taurari goma sha ɗaya suna rusuna mini.”
10 And when he had related this to his father and brothers, his father rebuked him, and he said: “What does it mean to you, this dream that you have seen? Should I, and your mother, and your brothers reverence you upon the earth?”
Sa’ad da ya faɗa wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa, sai mahaifinsa ya kwaɓe shi ya ce, “Wanne irin mafarki ne haka da ka yi? Kana nufin ni da mahaifiyarka da’yan’uwanka za mu zo gabanka mu rusuna maka?”
11 Therefore, his brothers were envious of him. Yet truly, his father considered the matter silently.
’Yan’uwansa suka yi kishinsa, amma mahaifinsa ya riƙe batun nan a zuciya.
12 And while his brothers were lodging at Shechem, pasturing their father’s flocks,
To,’yan’uwansa suka tafi kiwon garkunan mahaifinsu kusa da Shekem.
13 Israel said to him: “Your brothers are pasturing the sheep at Shechem. Come, I will send you to them.” And when he answered,
Sai Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Kamar yadda ka sani,’yan’uwanka suna kiwon garkuna kusa da Shekem. Zo, in aike ka gare su.” Ya ce, “To.”
14 “I am ready,” he said to him, “Go, and see if everything is prospering with your brothers and the cattle, and report to me what is happening.” So, having been sent from the valley of Hebron, he arrived at Shechem.
Saboda haka Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Jeka ka ga ko kome lafiya yake da’yan’uwanka da kuma garkunan, ka kawo mini labari.” Sa’an nan ya sallame shi daga Kwarin Hebron. Sa’ad da Yusuf ya kai Shekem,
15 And a man found him wandering in a field, and he asked him what he was seeking.
sai wani mutum ya same shi yana yawo a cikin jeji, sai mutumin ya tambaye shi ya ce, “Me kake nema?”
16 So he responded: “I seek my brothers. Tell me where they pasture the flocks.”
Yusuf ya amsa ya ce, “Ina neman’yan’uwana ne. Za ka iya faɗa mini inda suke kiwon garkunansu?”
17 And the man said to him: “They have withdrawn from this place. But I heard them saying, ‘Let us go to Dothan.’” Therefore, Joseph continued on after his brothers, and he found them at Dothan.
Mutumin ya amsa, “Sun yi gaba daga nan. Na ji su suna cewa, ‘Bari mu je Dotan.’” Saboda haka Yusuf ya bi bayan’yan’uwansa, ya kuwa same su kusa da Dotan.
18 And, when they had seen him from afar, before he approached them, they decided to kill him.
Amma da suka gan shi daga nesa, kafin yă kai wurinsu, sai suka ƙulla su kashe shi.
19 And they said one to another: “Behold, the dreamer approaches.
Suka ce wa juna, “Ga mai mafarkin nan can zuwa!
20 Come, let us kill him and cast him into the old cistern. And let us say: ‘an evil wild beast has devoured him.’ And then it will become apparent what his dreams will do for him.”
Ku zo mu kashe shi mu kuma jefa shi a ɗaya daga cikin rijiyoyin nan, mu ce mugun naman jeji ya cinye shi. Mu ga yadda mafarkinsa zai cika.”
21 But Reuben, on hearing this, strove to free him from their hands, and he said:
Sa’ad da Ruben ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă cece shi daga hannuwansu. Ya ce, “Kada mu ɗauki ransa.
22 “Do not take away his life, nor shed blood. But throw him into this cistern, which is in the wilderness, and so keep your hands harmless.” But he said this, wanting to rescue him from their hands, so as to return him to his father.
Kada mu zub da wani jini. Mu dai jefa shi cikin wannan rijiya a nan cikin hamada, amma kada mu sa hannu a kansa.” Ruben ya faɗa wannan ne don yă cece shi daga gare su, yă kuma mai da shi ga mahaifinsa.
23 And so, as soon as he came to his brothers, they very quickly stripped him of his tunic, which was ankle-length and woven of many colors,
Saboda haka sa’ad da Yusuf ya zo wurin’yan’uwansa, sai suka tuɓe masa rigarsa, rigan nan mai gwanin kyau da ya sa,
24 and they cast him into an old cistern, which held no water.
suka kuma ɗauke shi suka jefa a cikin rijiya. To, rijiyar wofi ce, babu ruwa a ciki.
25 And sitting down to eat bread, they saw some Ishmaelites, travelers coming from Gilead, with their camels, carrying spices, and resin, and oil of myrrh into Egypt.
Da suka zauna don cin abinci, sai suka tā da idanu, suka ga ayarin mutanen Ishmayel suna zuwa daga Gileyad. An yi wa raƙumansu labtu da kayan yaji da na ƙanshi, suna kan hanyarsu za su Masar.
26 Therefore, Judah said to his brothers: “What will it profit us, if we kill our brother and conceal his blood?
Yahuda ya ce wa’yan’uwansa, “Me zai amfane mu in muka kashe ɗan’uwanmu muka ɓoye jininsa?
27 It is better that he be sold to the Ishmaelites, and then our hands will not be defiled. For he is our brother and our flesh.” His brothers agreed to his words.
Ku zo, mu sayar da shi wa mutanen Ishmayelawan nan, kada mu sa hannuwanmu a kansa; ban da haka ma, shi ɗan’uwanmu ne, jiki da jininmu.” Sai’yan’uwansa suka yarda.
28 And when the Midianite merchants were passing by, they drew him from the cistern, and they sold him to the Ishmaelites for twenty pieces of silver. And these led him into Egypt.
Saboda haka sa’ad da Fataken Midiyawa suka iso, sai’yan’uwansa suka ja Yusuf daga rijiyar, suka sayar da shi a bakin shekel ashirin na azurfa wa mutanen Ishmayel, waɗanda suka ɗauke shi zuwa Masar.
29 And Reuben, returning to the cistern, did not find the boy.
Sa’ad da Ruben ya dawo wurin rijiyar, sai ya tarar cewa Yusuf ba ya can, sai ya kyakkece tufafinsa.
30 And rending his garments, he went to his brothers and said, “The boy is not present, and so where shall I go?”
Ya koma wurin’yan’uwansa ya ce, “Yaron ba ya can! Ina zan bi yanzu?”
31 Then they took his tunic, and they dipped it in the blood of a young goat, which they had killed,
Sai suka ɗauki rigar Yusuf, suka yanka akuya suka tsoma rigar a cikin jinin.
32 sending those who carried it to their father, and they said: “We found this. See whether it is the tunic of your son or not.”
Suka ɗauki rigan nan mai gwanin kyau, suka kawo wa mahaifinsu suka ce, “Mun sami wannan. Ka bincika shi ka gani ko rigar ɗanka ne.”
33 And when the father acknowledged it, he said: “It is the tunic of my son. An evil wild beast has eaten him; a beast has devoured Joseph.”
Ya gane shi, sai ya ce, “Rigar ɗana ne! Waɗansu mugayen namun jeji sun cinye shi. Tabbatacce an yayyaga Yusuf.”
34 And tearing his garments, he was clothed in haircloth, mourning his son for a long time.
Sa’an nan Yaƙub ya kyakkece tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya kuma yi makoki domin ɗansa kwanaki masu yawa.
35 Then, when all of his sons gathered together to ease their father’s sorrow, he was not willing to accept consolation, but he said: “I will descend in mourning to my son in the underworld.” And while he persevered in weeping, (Sheol h7585)
Dukan’ya’yansa maza da mata, suka zo don su ta’azantar da shi, amma ya ƙi yă ta’azantu. Ya ce, “A’a, cikin makoki zan gangara zuwa kabari wurin ɗana.” Saboda haka, mahaifin Yusuf ya yi kuka saboda shi. (Sheol h7585)
36 the Midianites in Egypt sold Joseph to Potiphar, a eunuch of Pharaoh, instructor of the soldiers.
Ana cikin haka, Midiyawa suka sayar da Yusuf a Masar wa Fotifar, ɗaya daga cikin shugabannin’yan gadin fadar Fir’auna.

< Genesis 37 >