< Genesis 36 >

1 Now these are the generations of Esau, who is Edom.
Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom).
2 Esau took wives from the daughters of Canaan: Adah the daughter of Elon the Hittite, and Oholibamah the daughter of Anah, the daughter of Zibeon the Hivite,
Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye
3 and Basemath, the daughter of Ishmael, sister of Nebaioth.
ya kuma auri Basemat’yar Ishmayel wadda take’yar’uwar Nebayiwot.
4 Then Adah bore Eliphaz. Basemath conceived Reuel.
Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel.
5 Oholibamah conceived Jeush, and Jalam, and Korah. These are the sons of Esau, who were born to him in the land of Canaan.
Oholibama kuwa ta haifa masa Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza, waɗanda aka haifa masa a Kan’ana.
6 Then Esau took his wives, and sons, and daughters, and every soul of his house, and his substance, and cattle, and whatever he was able to obtain in the land of Canaan, and he went into another region, withdrawing from his brother Jacob.
Isuwa ya ɗauki matansa da’ya’yansa maza da mata da kuma dukan membobin gidansa, ya kuma ɗauki shanunsa da dukan sauran dabbobinsa, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan’ana zuwa wata ƙasa nesa da ɗan’uwansa Yaƙub.
7 For they were very wealthy and were not able to live together. Neither was the land of their sojourn able to sustain them, because of the multitude of their flocks.
Mallakarsu ta yi yawa ƙwarai da ba za su iya zauna tare ba; gama ƙasar da suke zaune a ciki ba za tă ishe su su biyu ba saboda dabbobinsu.
8 And Esau lived at mount Seir: he is Edom.
Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir.
9 So these are the generations of Esau, the father of Edom, at mount Seir,
Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir.
10 and these are the names of his sons: Eliphaz the son of Adah, the wife of Esau, likewise Reuel, the son of Basemath, his wife.
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa.
11 And Eliphaz had sons: Teman, Omar, Zepho, and Gatam, and Kenez.
’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz.
12 Now Timna was the concubine of Eliphaz, the son of Esau. And she bore him Amalek. These are the sons of Adah, the wife of Esau.
Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa.
13 And the sons of Reuel were Nahath and Zerah, Shammah and Mizzah. These are the sons of Basemath, the wife of Esau.
’Ya’yan Reyuwel maza su ne, Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
14 Likewise, these were the sons of Oholibamah, the daughter of Anah, the daughter of Zibeon, the wife of Esau, whom she bore to him: Jeush, and Jalam, and Korah.
’Ya’yan Oholibama maza’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon, matar Isuwa, waɗanda ta haifa wa Isuwa su ne, Yewush, Yalam da Kora.
15 These were leaders of the sons of Esau, the sons of Eliphaz, the firstborn of Esau: leader Teman, leader Omar, leader Zepho, leader Kenez,
Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa,’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz,
16 leader Korah, leader Gatam, leader Amalek. These are the sons of Eliphaz, in the land of Edom, and these the sons of Adah.
Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada.
17 Likewise, these are the sons of Reuel, the son of Esau: leader Nahath, leader Zerah, leader Shammah, leader Mizzah. And these were the leaders of Reuel, in the land of Edom. These are the sons of Basemath, the wife of Esau.
’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
18 Now these are the sons of Oholibamah, the wife of Esau: leader Jeush, leader Jalam, leader Korah. These were the leaders of Oholibamah, the daughter of Anah and the wife of Esau.
’Ya’yan Oholibama maza matar Isuwa, Shugabannin su ne; Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Oholibama’yar Ana matar Isuwa.
19 These are the sons of Esau, and these were their leaders: this is Edom.
Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu.
20 These are the sons of Seir, the Horite, the inhabitants of the land: Lotan, and Shobal, and Zibeon, and Anah,
Waɗannan su ne’ya’yan Seyir Bahore maza, waɗanda suke zaune a yankin, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
21 and Dishon, and Ezer, and Dishan. These were the leaders of the Horites, the sons of Seir, in the land of Edom.
Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa,’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom.
22 Now Lotan produced sons: Hori and Heman. But the sister of Lotan was Timna.
’Ya’yan Lotan maza su ne, Hori da Homam. Timna’yar’uwar Lotan ce.
23 And these are the sons of Shobal: Alvan, and Manahath, and Ebal, and Shepho, and Onam.
’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam.
24 And these are the sons of Zibeon: Aiah and Anah. This is the Anah who found the hot springs in the wilderness, when he was pasturing the donkeys of his father Zibeon.
’Ya’yan Zibeyon maza su ne, Aiya da Ana. Wannan shi ne Ana wanda ya sami maɓulɓulan ruwan zafi a hamada yayinda yake kiwon jakuna na mahaifinsa Zibeyon.
25 And he had a son Dishon, and a daughter Oholibamah.
’Ya’yan Ana su ne, Dishon da Oholibama’yar Ana.
26 And these are the sons of Dishon: Hemdan, and Esheban, and Ithran, and Cheran.
’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran.
27 Likewise, these are the sons of Ezer: Bilhan, and Zaavan, and Akan.
’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan.
28 Then Dishan had sons: Uz and Aran.
’Ya’yan Dishan maza su ne, Uz da Aran.
29 These were the leaders of the Horites: leader Lotan, leader Shobal, leader Zibeon, leader Anah,
Waɗannan su ne manyan Horiyawa, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
30 leader Dishon, leader Ezer, leader Disan. These were leaders of the Horites who ruled in the land of Seir.
Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir.
31 Now before the sons of Israel had a king, the kings who ruled in the land of Edom were these:
Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki,
32 Bela the son of Beor, and the name of his city was Dinhabah.
Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba.
33 Then Bela died, and Jobab, the son of Zerah from Bozrah, reigned in his place.
Sa’ad da Bela ya rasu, Yobab ɗan Zera daga Bozra ya gāje shi.
34 And when Jobab was dead, Husham of the land of the Temanites reigned in his place.
Sa’ad da Yobab ya rasu, Husham daga ƙasar Temaniyawa ya gāje shi.
35 Likewise, this one having died, Hadad the son of Bedad reigned in his place. He struck down Midian in the region of Moab. And the name of his city was Avith.
Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
36 And when Adad was dead, Samlah of Masrekah reigned in his place.
Sa’ad da Hadad ya rasu, Samla daga Masreka ya gāje shi.
37 Likewise, this one being dead, Shaul of the river Rehoboth, reigned in his place.
Sa’ad da Samla ya rasu, Sha’ul daga Rehobot na ta kogi ya gāje shi.
38 And when he also had passed away, Baal-hanan, the son of Achbor, succeeded to the kingdom.
Sa’ad da Sha’ul ya rasu, Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya gāje shi.
39 Likewise, this one being dead, Hadar reigned in his place; and the name of his city was Pau. And his wife was called Mehetabel, the daughter of Matred, daughter of Mezahab.
Sa’ad da Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya rasu, Hadad ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Fau, kuma sunan matarsa Mehetabel ce’yar Matired, jikanyar Me-Zahab.
40 Therefore, these were the names of the leaders of Esau, by their families, and places, and in their vocabulary: leader Timna, leader Alvah, leader Jetheth,
Waɗannan su ne manya da suka fito daga zuriyar Isuwa, bisa ga danginsu, bisa kuma ga kabilansu da yankunansu. Sunayensu su ne, Timna, Alwa, Yetet.
41 leader Oholibamah, leader Elah, leader Pinon,
Oholibama, Ela, Finon.
42 leader Kanez, leader Teman, leader Mibzar,
Kenaz, Teman, Mibzar.
43 leader Magdiel, leader Iram. These were the leaders of Edom living in the land of their rule: this is Esau, the father of Idumea.
Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom.

< Genesis 36 >