< Genesis 35 >

1 About this time, God said to Jacob, “Arise and go up to Bethel, and live there, and make an altar to God, who appeared to you when you fled from your brother Esau.”
Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
2 In truth, Jacob, having called together all his house, said: “Cast away the foreign gods that are in your midst and be cleansed, and also change your garments.
Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
3 Arise, and let us go up to Bethel, so that we may make an altar there to God, who heeded me in the day of my tribulation, and who accompanied me on my journey.”
Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
4 Therefore, they gave him all the foreign gods which they had, and the earrings which were in their ears. And then he buried them under the terebinth tree, which is beyond the city of Shechem.
Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
5 And when they had set out, the terror of God invaded all the surrounding cities, and they dared not pursue them as they withdrew.
Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
6 And so, Jacob arrived at Luz, which is in the land of Canaan, also named Bethel: he and all the people with him.
Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
7 And he built an altar there, and he called the name of that place, ‘House of God.’ For there, God appeared to him when he fled from his brother.
A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
8 About the same time, Deborah, the nurse of Rebekah, died, and she was buried at the base of Bethel, under an oak tree. And the name of that place was called, ‘Oak of Weeping.’
To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
9 Then God appeared again to Jacob, after he returned from Mesopotamia of Syria, and he blessed him,
Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
10 saying: “You will no longer be called Jacob, for your name shall be Israel.” And he called him Israel,
Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
11 and he said to him: “I am Almighty God: increase and multiply. Tribes and peoples of nations will be from you, and kings will go forth from your loins.
Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
12 And the land that I gave to Abraham and Isaac, I will give to you, and to your offspring after you.”
Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
13 And he withdrew from him.
Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
14 In truth, he set up a monument of stone, in the place where God had spoken to him, pouring out libations over it, and pouring oil,
Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
15 and he called the name of that place, ‘Bethel.’
Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
16 Then, departing from there, he arrived in springtime at the land that leads to Ephrath. And there, when Rachel was giving birth,
Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
17 because it was a difficult birth, she began to be in danger. And the midwife said to her, “Do not be afraid, for you will have this son also.”
Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
18 Then, when her life was departing because of the pain, and death was now imminent, she called the name of her son Benoni, that is, the son of my pain. Yet truly, his father called him Benjamin, that is, the son of the right hand.
Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
19 And so Rachel died, and she was buried in the way that leads to Ephrath: this place is Bethlehem.
Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
20 And Jacob erected a monument over her sepulcher. This is the monument to Rachel’s tomb, even to the present day.
Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
21 Departing from there, he pitched his tent beyond the Tower of the Flock.
Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
22 And when he was living in that region, Reuben went out, and he slept with Bilhah the concubine of his father, which was not such a small matter as to be hidden from him. Now the sons of Jacob were twelve.
Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
23 The sons of Leah: Reuben the first born, and Simeon, and Levi, and Judah, and Issachar, and Zebulun.
’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
24 The sons of Rachel: Joseph and Benjamin.
’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
25 The sons of Bilhah, handmaid of Rachel: Dan and Naphtali.
’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
26 The sons of Zilpah, handmaid of Leah: Gad and Asher. These are the sons of Jacob, who were born to him in Mesopotamia of Syria.
’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
27 And then he went to his father Isaac in Mamre, the city of Arba: this place is Hebron, where Abraham and Isaac sojourned.
Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
28 And the days of Isaac were completed: one hundred and eighty years.
Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
29 And being consumed by old age, he died. And he was placed with his people, being old and full of days. And his sons, Esau and Jacob, buried him.
sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.

< Genesis 35 >