< Genesis 31 >

1 But afterwards, he heard the words of the sons of Laban, saying, “Jacob has taken all that was our father’s, and being enlarged by his ability, he has become famous.”
Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
2 Likewise, he observed that Laban’s face was not the same toward him as it was yesterday and the day before.
Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
3 Most importantly, the Lord was saying to him, “Return to the land of your fathers and to your generation, and I will be with you.”
Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
4 He sent and called for Rachel and Leah, in the field where he pastured the flocks,
Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
5 and he said to them: “I see that your father’s face is not the same toward me as it was yesterday and the day before. But the God of my father has been with me.
Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
6 And you know that I have served your father with all my strength.
Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
7 Even so, your father has circumvented me, and he has changed my wages ten times. And yet God has not permitted him to harm me.
duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
8 Whenever he said, ‘The speckled will be your wages,’ all the sheep gave birth to speckled newborns. Yet truly, when he said the contrary, ‘You will take whatever is white for your wages,’ all the flocks gave birth to white ones.
In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
9 And it is God who has taken your father’s substance and given it to me.
Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
10 For after the time had arrived for the ewes to conceive, I lifted up my eyes, and I saw in my sleep that the males climbing on the females were of variegated, and spotted, and diverse colors.
“A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
11 And the Angel of God said to me in my sleep, ‘Jacob.’ And I responded, ‘Here I am.’
Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
12 And he said: ‘Lift up your eyes, and see that all the males climbing on the females are variegated, spotted, and also speckled. For I have seen all that Laban has done to you.
Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
13 I am the God of Bethel, where you anointed the stone and made a vow to me. Now therefore arise, and depart from this land, returning to the land of your nativity.’”
Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
14 And Rachel and Leah responded: “Have we anything left behind among the resources and inheritance of our father’s house?
Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
15 Has he not considered us as foreigners, and sold us, and consumed our price?
Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
16 But God has taken our father’s riches and handed these to us and to our sons. Therefore, do all that God has instructed you.”
Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
17 And so Jacob rose up, and having placed the children and his wives upon camels, he went forth.
Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
18 And he took all his substance and flocks, and whatever he had acquired in Mesopotamia, and he journeyed to his father Isaac, in the land of Canaan.
ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
19 At that time, Laban had gone to shear the sheep, and so Rachel stole her father’s idols.
Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
20 And Jacob was not willing to confess to his father-in-law that he was fleeing.
Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
21 And when he had gone away with all such things that were justly his, and, having crossed the river, was continuing on toward Mount Gilead,
Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
22 it was reported to Laban on the third day that Jacob had fled.
A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
23 And taking his brothers with him, he pursued him for seven days. And he overtook him at Mount Gilead.
Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
24 And he saw in a dream, God saying to him, “Beware that you not speak anything harsh against Jacob.”
Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
25 And now Jacob had pitched his tent at the mountain. And when he, with his brothers, had overtaken him, he set his tent at the same place at Mount Gilead.
Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
26 And he said to Jacob: “Why have you acted this way, departing from me in secret, with my daughters like captives of the sword?
Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
27 Why would you want to flee without my knowledge and without telling me, though I might have led you forward with gladness, and songs, and timbrels, and lyres?
Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
28 You have not permitted me to kiss my sons and daughters. You have acted foolishly. And now, indeed,
Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
29 my hand has power to repay you with harm. But the God of your father said to me yesterday, ‘Beware that you not speak anything stern against Jacob.’
Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
30 It may be that you desired to go to your own, and that you longed for the house of your father. But why have you stolen my gods?”
Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
31 Jacob answered: “I set out, unknown to you, because I feared that you might take away your daughters by violence.
Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
32 But, since you accuse me of theft, with whomever you will find your gods, let him be slain in the sight of our brothers. Search; anything of yours that you will find with me, take it away.” Now when he said this, he did not know that Rachel had stolen the idols.
Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
33 And so Laban, entering the tent of Jacob, and of Leah, and of both the handmaids, did not find them. And when he had entered the tent of Rachel,
Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
34 she quickly hid the idols under the camel’s bedding, and she sat upon them. And when he had searched the entire tent and found nothing,
Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
35 she said: “Do not be angry, my lord, that I am unable to rise up in your sight, because it has now happened to me according to the custom of women.” So his careful search was thwarted.
Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
36 And Jacob, being inflated, said with contention: “For which fault of mine, or for what sin of mine, have you become so enraged against me
Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
37 and searched all the items of my house? What have you found from all the substance of your house? Place it here before my brothers, and your brothers, and let them judge between me and you.
Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
38 For what reason have I been with you for twenty years? Your ewes and she-goats were not barren; the rams of your flocks I did not consume.
“Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
39 Neither did I reveal to you what was seized by the wild beast. I replaced all that was damaged. Whatever was lost by theft, you collected it from me.
Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
40 Day and night, I was burned by heat and by frost, and sleep fled from my eyes.
Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
41 And in this way, for twenty years, I have served you in your house: fourteen for your daughters, and six for your flocks. You have also changed my wages ten times.
Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
42 If the God of my father Abraham and the fear of Isaac had not been close to me, perhaps by now you would have sent me away naked. But God looked kindly on my affliction and the labor of my hands, and he rebuked you yesterday.”
Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
43 Laban answered him: “My daughters and sons, and your flocks, and all that you discern are mine. What can I do to my sons and grandchildren?
Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
44 Come, therefore, let us enter into a pact, so that it may be a testimony between me and you.”
Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
45 And so Jacob took a stone, and he set it up as a memorial.
Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
46 And he said to his brothers, “Bring stones.” And they, gathering together stones, made a tomb, and they ate upon it.
Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
47 And Laban called it, ‘Tomb of Witness,’ and Jacob, ‘Pile of Testimony;’ each of them according to the fitness of his own language.
Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
48 And Laban said: “This tomb will be a witness between me and you this day.” (And for this reason, its name has been called Gilead, that is, ‘Tomb of Witness.’)
Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
49 “May the Lord consider and judge between us, when we will have withdrawn from one another.
Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
50 If you afflict my daughters, and if you bring in other wives over them, no one is a witness of our words except God, who understands beforehand.”
Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
51 And again he said to Jacob. “Lo, this tomb and the stone that I have set up between me and you,
Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
52 will be a witness. This tomb,” I say, “and the stone, they are for testimony, in case either I cross beyond it going toward you, or you cross beyond it thinking to harm me.
Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
53 May the God of Abraham, and the God of Nahor, the God of their father, judge between us.” Therefore, Jacob swore by the fear of his father Isaac.
Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
54 And after he had immolated sacrifices on the mountain, he called his brothers to eat bread. And when they had eaten, they lodged there.
Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
55 In truth, Laban rose up in the night, and he kissed his sons and daughters, and he blessed them. And he returned to his place.
Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.

< Genesis 31 >