< Genesis 27 >

1 Now Isaac was old, and his eyes were cloudy, and so he was not able to see. And he called his elder son Esau, and he said to him, “My son?” And he responded, “Here I am.”
Sa’ad da Ishaku ya tsufa idanunsa suka raunana har ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa babban ɗansa ya ce masa, “Ɗana.” Isuwa kuwa ya amsa, ya ce “Ga ni.”
2 His father said to him: “You see that I am old, and I do not know the day of my death.
Ishaku ya ce, “Yanzu na tsufa kuma ban san ranar mutuwata ba.
3 Take your weapons, the quiver and the bow, and go out. And when you have taken something by hunting,
Saboda haka yanzu, ka ɗauki makamanka, kwari da bakanka, ka tafi jeji ka farauto mini nama.
4 make from it a small meal for me, just as you know I like, and bring it, so that I may eat and my soul may bless you before I die.”
Ka shirya mini irin abinci mai daɗin da nake so, ka kawo mini in ci, domin in sa maka albarka kafin in mutu.”
5 And when Rebekah had heard this, and he had gone out into the field to fulfill his father’s order,
Ashe, Rebeka tana ji sa’ad da Ishaku ya yi wa ɗansa Isuwa magana. Da Isuwa ya tafi jeji don yă farauto nama yă kawo,
6 she said to her son Jacob: “I heard your father speaking with your brother Esau, and saying to him,
sai Rebeka ta ce wa ɗanta Yaƙub, “Ka ji nan, na ji mahaifinka ya ce wa ɗan’uwanka Isuwa,
7 ‘Bring to me from your hunting, and make me foods, so that I may eat and bless you in the sight of the Lord before I die.’
‘Kawo mini nama ka shirya mini abinci mai daɗi don in ci, in sa maka albarka a gaban Ubangiji kafin in mutu.’
8 Therefore, now my son, agree to my counsel,
Saboda haka ɗana, ka saurara da kyau ka kuma yi abin da na faɗa maka.
9 and go straight to the flock, and bring me two of the best young goats, so that from them I may make meat for your father, such as he willingly eats.
Je garke ka kawo mini awaki biyu kyawawa, domin in shirya abinci mai daɗi wa mahaifinka, kamar yadda dai yake so.
10 Then, when you have brought these in and he has eaten, he may bless you before he dies.”
Sa’an nan ka kai wa mahaifinka yă ci, domin yă sa maka albarka kafin yă mutu.”
11 He answered her: “You know that my brother Esau is a hairy man, and I am smooth.
Yaƙub ya ce wa mahaifiyarsa Rebeka, “Amma ɗan’uwana Isuwa mutum ne mai gashi a jiki, ni kuma jikina sumul yake.
12 If my father should lay hands on me and perceive it, I am afraid lest he think me willing to mock him, and I will bring a curse upon myself, instead of a blessing.”
A ce baba ya tattaɓa ni fa? Zai zama kamar ina ruɗunsa ne, wannan fa zai jawo mini la’ana a maimakon albarka.”
13 And his mother said to him: “Let this curse be upon me, my son. Yet listen to my voice, and go directly to bring what I said.”
Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, bari la’anar tă fāɗo a kaina. Kai dai yi abin da na faɗa, jeka ka kawo mini su.”
14 He went out, and he brought, and he gave to his mother. She prepared the meats, just as she knew his father liked.
Sai ya tafi ya kamo su, ya kawo wa mahaifiyarsa, ta kuwa shirya abinci mai daɗi, yadda mahaifinsa yake so.
15 And she clothed him with the very fine garments of Esau, which she had at home with her.
Sa’an nan Rebeka ta ɗauki riguna mafi kyau na Isuwa babban ɗanta, waɗanda take da su a gida ta sa wa ƙaramin ɗanta Yaƙub.
16 And she encircled his hands with little pelts from the young goats, and she covered his bare neck.
Sai ta mamanne gashin awakin nan biyu a hannuwansa da bayan wuyarsa wanda ba gashi.
17 And she gave him the small meal, and she handed him the bread that she had baked.
Sa’an nan ta ba wa ɗanta Yaƙub abinci mai daɗi da kuma burodin da ta yi.
18 When he had carried these in, he said, “My father?” And he answered, “I’m listening. Who are you, my son?”
Shi kuwa ya tafi wurin mahaifinsa ya ce, “Babana.” Shi kuma ya amsa “I, ɗana, wane ne?”
19 And Jacob said: “I am Esau, your firstborn. I have done as you instructed me. Arise; sit and eat from my hunting, so that your soul may bless me.”
Yaƙub ya ce wa mahaifinsa, “Ni ne Isuwa ɗan farinka. Na yi yadda ka faɗa mini. Ina roƙonka tashi ka zauna ka ci naman, domin ka sa mini albarkarka.”
20 And again Isaac said to his son, “How were you able to find it so quickly, my son?” He answered, “It was the will of God, so that what I sought met with me quickly.”
Ishaku ya tambayi ɗansa, “Yaya aka yi ka samo shi da sauri haka, ɗana?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Ubangiji Allahnka ne ya ba ni nasara.”
21 And Isaac said, “Come here, so that I may touch you, my son, and may prove whether you are my son Esau, or not.”
Sai Ishaku ya ce wa Yaƙub, “Zo kusa don in taɓa ka, ɗana, domin in sani ko tabbatacce kai ne ɗana Isuwa ko babu.”
22 He approached his father, and when he had felt him, Isaac said: “The voice indeed is the voice of Jacob. But the hands are the hands of Esau.”
Yaƙub kuwa ya matsa kusa da mahaifinsa Ishaku, wanda ya tattaɓa shi, sa’an nan ya ce, “Muryan nan dai, muryar Yaƙub ce, amma hannuwan, hannuwan Isuwa ne.”
23 And he did not recognize him, because his hairy hands made him seem similar to the elder one. Therefore, blessing him,
Bai gane shi ba, gama hannuwansa suna da gashi kamar na ɗan’uwansa Isuwa, saboda haka ya albarkace shi.
24 he said, “Are you my son Esau?” He answered, “I am.”
Ya tambaya, “Tabbatacce kai ne ɗana Isuwa?” Ya amsa ya ce “Ni ne.”
25 Then he said, “Bring me the foods from your hunting, my son, so that my soul may bless you.” And when he had eaten what was offered, he also brought forth wine for him. And after he finished it,
Sa’an nan ya ce, “Ɗana, kawo mini naman da ka farauto in ci, domin in sa maka albarka.” Yaƙub ya kawo masa ya kuwa ci; ya kuma kawo masa ruwan inabi ya kuma sha.
26 he said to him, “Come to me and give me a kiss, my son.”
Sa’an nan mahaifinsa Ishaku ya ce masa, “Zo nan, ɗana ka sumbace ni.”
27 He approached and kissed him. And immediately he perceived the fragrance of his garments. And so, blessing him, he said: “Behold, the smell of my son is like the smell of a plentiful field, which the Lord has blessed.
Saboda haka ya je gunsa ya sumbace shi. Sa’ad da Ishaku ya ji ƙanshin rigunansa, sai ya sa masa albarka ya ce, “Aha, ƙanshin ɗana yana kama da ƙanshin jejin da Ubangiji ya sa wa albarka ne.
28 May God give to you, from the dew of heaven and from the fatness of the earth, an abundance of grain and wine.
Allah yă ba ka daga raɓar sama da kuma yalwar ƙasa, yalwar hatsi da sabon ruwan inabi.
29 And may the peoples serve you, and may the tribes reverence you. May you be the lord of your brothers, and may your mother’s sons bow down before you. Whoever curses you, may he be cursed, and whoever blesses you, may he be filled with blessings.”
Bari al’ummai su bauta maka mutane kuma su rusuna maka. Ka zama shugaba a kan’yan’uwanka bari kuma’ya’yan mahaifiyarka su rusuna maka. Bari waɗanda suka la’anta ka, su la’antu; waɗanda kuma suka sa maka albarka, su sami albarka.”
30 Scarcely had Isaac completed his words, and Jacob departed, when Esau arrived.
Bayan Ishaku ya gama sa masa albarka, Yaƙub yana fita daga mahaifinsa ke nan, sai ga ɗan’uwansa Isuwa ya dawo daga farauta.
31 And he brought his father foods cooked from his hunting, saying, “Arise, my father, and eat from your son’s hunting, so that your soul may bless me.”
Shi ma ya shirya abinci mai daɗi ya kawo wa mahaifinsa. Sa’an nan ya ce masa, “Babana, tashi ka zauna ka ci daga abin da na farauto, domin ka sa mini albarka.”
32 And Isaac said to him, “But who are you?” And he answered, “I am your firstborn son, Esau.”
Mahaifinsa Ishaku ya tambaye shi, “Wane ne kai?” Ya amsa, “Ni ne ɗanka, ɗan farinka, Isuwa.”
33 Isaac became frightened and very astonished. And wondering beyond what can be believed, he said: “Then who is he that a while ago brought me the prey from his hunting, from which I ate, before you arrived? And I blessed him, and he will be blessed.”
Ishaku ya yi makyarkyata ƙwarai ya ce, “To, wane ne wannan da ya farauto nama ya kawo mini kafin ka zo, har na ci na kuma sa masa albarka? Tabbatacce zai zama mai albarka!”
34 Esau, having heard his father’s words, roared out with a great outcry. And, being confounded, he said, “But bless me also, my father.”
Sa’ad da Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, sai ya fashe da kuka mai zafi kuma da ƙarfi, ya ce wa mahaifinsa, “Ka albarkace ni, ni ma, baba!”
35 And he said, “Your twin came deceitfully, and he received your blessing.”
Amma ya ce, “Ɗan’uwanka ya zo da makirci ya karɓi albarkarka.”
36 But he responded: “Justly is his name called Jacob. For he has supplanted me yet another time. My birthright he took away before, and now, this second time, he has stolen my blessing.” And again, he said to his father, “Have you not reserved a blessing for me also?”
Isuwa ya ce, “Ba saboda haka ne aka raɗa masa suna Yaƙub ba? Ya yi mini ƙwace sau biyu ke nan; ya ƙwace mini matsayina na ɗan fari, ga shi yanzu kuma ya karɓi albarkata.” Sa’an nan ya yi tambaya, “Ba sauran albarkar da ka rage mini?”
37 Isaac answered: “I have appointed him as your lord, and I have subjugated all his brothers as his servants. I have reinforced him with grain and wine, and after this, my son, what more shall I do for you?”
Ishaku ya amsa wa Isuwa, “Na mai da shi shugaba a kanka, na sa dukan dangoginsa su zama bayinsa, na kuma ba shi hatsi da sabon ruwan inabi. Saboda haka me kuma zan yi maka ɗana?”
38 And Esau said to him: “Have you only one blessing, father? I beg you, bless me also.” And when he wept with a loud wail,
Isuwa ya ce wa mahaifinsa, “Iyakar albarkar da kake da ita ke nan, baba? Ka albarkace ni ni ma, baba!” Sai Isuwa ya ɗaga murya ya yi kuka.
39 Isaac was moved, and he said to him: “In the fatness of the earth, and in the dew of heaven from above,
Mahaifinsa Ishaku ya amsa masa ya ce, “Ga shi, ni’imar ƙasar za tă nisanci mazauninka. Raɓar samaniya can ƙwanƙoli za tă nisance ka.
40 will your blessing be. You will live by the sword, and you will serve your brother. But the time will arrive when you will shake off and release his yoke from your neck.”
Za ka rayu ta wurin takobi za ka kuwa bauta wa ɗan’uwanka. Amma sa’ad da ka ɓalle, za ka kakkarye karkiyarsa daga wuyanka.”
41 Therefore, Esau always hated Jacob, for the blessing with which his father had blessed him. And he said in his heart, “The days will arrive for the mourning of my father, and I will kill my brother Jacob.”
Isuwa ya riƙe Yaƙub a zuciya saboda albarkar da mahaifinsa ya sa masa. Ya ce wa kansa, “Kwanakin mutuwar mahaifina sun yi kusa; sa’an nan zan kashe ɗan’uwana Yaƙub.”
42 These things were reported to Rebekah. And sending and calling for her son Jacob, she said to him, “Behold, your brother Esau is threatening to kill you.
Sa’ad da aka faɗa wa Rebeka abin da babban ɗanta Isuwa ya faɗa, sai ta kira ɗanta Yaƙub ta ce masa, “Ɗan’uwanka Isuwa yana ta’azantar da kansa da tunanin kashe ka.
43 Therefore, now my son, listen to my voice. Rise up and flee to my brother Laban, in Haran.
To, fa, ɗana, yi abin da na ce; gudu nan take zuwa wurin ɗan’uwana Laban a Haran.
44 And you will dwell with him for a few days, until the fury of your brother subsides,
Zauna tare da shi na ɗan lokaci sai ɗan’uwanka ya huce.
45 and his indignation ceases, and he forgets the things that you have done to him. After this, I will send for you and bring you from there to here. Why should I be bereaved of both my sons in one day?”
Sa’ad da ɗan’uwanka ya daina fushi da kai, ya kuma manta da abin da ka yi masa, zan aika don ka dawo daga can. Don me zan rasa ku biyu a rana guda?”
46 And Rebekah said to Isaac, “I am weary of my life because of the daughters of Heth. If Jacob accepts a wife from the stock of this land, I would not be willing to live.”
Sa’an nan Rebeka ta ce wa Ishaku, “Ni fa na gaji da matan Hittiyawan nan. In Yaƙub ya auri mata daga cikin matan ƙasan nan, wato, daga matan Hittiyawa irin waɗannan, rayuwata ba za tă daɗa mini kome ba.”

< Genesis 27 >