< Genesis 2 >

1 And so the heavens and the earth were completed, with all their adornment.
Ta haka aka gama yin sammai da duniya da dukan abubuwan da suke cikinsu.
2 And on the seventh day, God fulfilled his work, which he had made. And on the seventh day he rested from all his work, which he had accomplished.
Kafin kwana ta bakwai, Allah ya gama aikin da yake yi, saboda haka a kwana ta bakwai, ya huta daga dukan aikinsa.
3 And he blessed the seventh day and sanctified it. For in it, he had ceased from all his work: the work whereby God created whatever he should make.
Allah kuwa ya albarkaci kwana ta bakwai, ya kuma mai da ita mai tsarki, saboda a kanta ne ya huta daga dukan aikin halittar da ya yi.
4 These are the generations of heaven and earth, when they were created, in the day when the Lord God made heaven and earth,
Wannan shi ne asalin tarihin sammai da duniya sa’ad da aka halicce su. Sa’ad da Ubangiji Allah ya yi duniya da sammai,
5 and every sapling of the field, before it would rise up in the land, and every wild plant, before it would germinate. For the Lord God had not brought rain upon the earth, and there was no man to work the land.
babu tsiro a duniya kuma ganyaye ba su tsira a busasshiyar ƙasa ko ba, gama Ubangiji Allah bai aiko da ruwan sama a kan duniya ba tukuna, babu kuma wani mutumin da zai nome ƙasar,
6 But a fountain ascended from the earth, irrigating the entire surface of the land.
amma dai rafuffuka suna ɓullo da ruwa daga ƙasa suna jiƙe ko’ina a fāɗin ƙasa.
7 And then the Lord God formed man from the clay of the earth, and he breathed into his face the breath of life, and man became a living soul.
Sa’an nan Ubangiji Allah ya yi mutum daga turɓayar ƙasa, ya kuma hura numfashin rai cikin hancinsa, mutumin kuwa ya zama rayayyen taliki.
8 Now the Lord God had planted a Paradise of enjoyment from the beginning. In it, he placed the man whom he had formed.
To, fa, Ubangiji Allah ya yi lambu a gabas, a Eden, a can kuwa ya sa mutumin da ya yi.
9 And from the soil the Lord God produced every tree that was beautiful to behold and pleasant to eat. And even the tree of life was in the midst of Paradise, and the tree of the knowledge of good and evil.
Ubangiji Allah ya kuma sa kowane irin itace ya tsira daga ƙasa, itace mai kyan gani, mai amfani kuma don abinci. A tsakiyar lambun kuwa akwai itacen rai da kuma itacen sanin abin da yake da kyau da abin da yake mugu.
10 And a river went forth from the place of enjoyment so as to irrigate Paradise, which is divided from there into four heads.
Akwai wani kogi mai ba da ruwa ga lambun wanda ya gangaro daga Eden, daga nan ya rarrabu, ya zama koguna huɗu.
11 The name of one is the Phison; it is that which runs through all the land of Hevilath, where gold is born;
Sunan kogi na fari, Fishon. Shi ne yake malala kewaye da dukan ƙasar Hawila, inda akwai zinariya.
12 and the gold of that land is the finest. In that place is found bdellium and the onyx stone.
(Zinariyar wannan ƙasa kuwa tana da kyau, akwai kuma kayan ƙanshi da duwatsun da ake kira onis a can ma.)
13 And the name of the second river is the Gehon; it is that which runs through all the land of Ethiopia.
Sunan kogi na biyu, Gihon. Shi ne ya malala kewaye da ƙasar Kush.
14 Truly, the name of the third river is the Tigris; it advances opposite the Assyrians. But the fourth river, it is the Euphrates.
Sunan kogi na uku Tigris. Wannan ne ya malala ya bi ta gefen gabashin Asshur. Kogi na huɗu kuwa shi ne Yuferites.
15 Thus, the Lord God brought the man, and put him into the Paradise of enjoyment, so that it would be attended and preserved by him.
Ubangiji Allah ya ɗauko mutumin ya sa shi cikin Lambun Eden domin yă nome shi, yă kuma lura da shi.
16 And he instructed him, saying: “From every tree of Paradise, you shall eat.
Ubangiji Allah ya umarci mutumin ya ce, “Kana da’yanci ka ci daga kowane itace a cikin lambun,
17 But from the tree of the knowledge of good and evil, you shall not eat. For in whatever day you will eat from it, you will die a death.”
amma kada ka ci daga itacen sanin abin da yake mai kyau da abin da yake mugu, gama a ranar da ka ci shi, lalle za ka mutu.”
18 The Lord God also said: “It is not good for the man to be alone. Let us make a helper for him similar to himself.”
Ubangiji Allah ya ce, “Bai yi kyau mutumin yă kasance shi kaɗai ba. Zan yi masa mataimakin da ya dace da shi.”
19 Therefore, the Lord God, having formed from the soil all the animals of the earth and all the flying creatures of the air, brought them to Adam, in order to see what he would call them. For whatever Adam would call any living creature, that would be its name.
To, Ubangiji Allah ya yi dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama daga ƙasa. Ya kawo su wurin mutumin don yă ga wanda suna zai kira su; kuma duk sunan da mutumin ya kira kowane mai rai, sunansa ke nan.
20 And Adam called each of the living things by their names: all the flying creatures of the air, and all the wild beasts of the land. Yet truly, for Adam, there was not found a helper similar to himself.
Saboda haka mutumin ya sa wa dukan dabbobi, da tsuntsayen sama da dukan namun jeji sunaye. Amma ba a sami mataimakin da ya dace da Adamu ba.
21 And so the Lord God sent a deep sleep upon Adam. And when he was fast asleep, he took one of his ribs, and he completed it with flesh for it.
Saboda haka Ubangiji Allah ya sa mutumin ya yi barci mai nauyi; yayinda yake barci sai ya ɗauko ɗaya daga cikin haƙarƙarin mutumin, ya kuma rufe wurin da nama.
22 And the Lord God built up the rib, which he took from Adam, into a woman. And he led her to Adam.
Sa’an nan Ubangiji Allah ya yi mace daga haƙarƙarin da ya ɗauko daga mutumin, ya kuwa kawo ta wurin mutumin.
23 And Adam said: “Now this is bone from my bones, and flesh from my flesh. This one shall be called woman, because she was taken from man.”
Sai mutumin ya ce, “Yanzu kam wannan ƙashi ne na ƙasusuwana nama kuma na namana. Za a ce da ita ‘mace,’ gama an ciro ta daga namiji.”
24 For this reason, a man shall leave behind his father and mother, and he shall cling to his wife; and the two shall be as one flesh.
Wannan ne ya sa mutum yakan bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa, su kuma zama jiki ɗaya.
25 Now they were both naked: Adam, of course, and his wife. And they were not ashamed.
Mutumin da matarsa, dukansu biyu tsirara suke, ba su kuwa ji kunya ba.

< Genesis 2 >