< Genesis 11 >

1 Now the earth was of one language and of the same speech.
To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
2 And when they were advancing from the east, they found a plain in the land of Shinar, and they dwelt in it.
Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
3 And each one said to his neighbor, “Come, let us make bricks, and bake them with fire.” And they had bricks instead of stones, and pitch instead of mortar.
Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
4 And they said: “Come, let us make a city and a tower, so that its height may reach to heaven. And let us make our name famous before we are divided into all the lands.”
Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
5 Then the Lord descended to see the city and the tower, which the sons of Adam were building.
Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
6 And he said: “Behold, the people are united, and all have one tongue. And since they have begun to do this, they will not desist from their plans, until they have completed their work.
Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
7 Therefore, come, let us descend, and in that place confound their tongue, so that they may not listen, each one to the voice of his neighbor.”
Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
8 And so the Lord divided them from that place into all the lands, and they ceased to build the city.
Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
9 And for this reason, its name was called ‘Babel,’ because in that place the language of the whole earth became confused. And from then on, the Lord scattered them across the face of every region.
Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
10 These are the generations of Shem. Shem was one hundred years old when he conceived Arphaxad, two years after the great flood.
Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
11 And after he conceived Arphaxad, Shem lived for five hundred years, and he conceived sons and daughters.
Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
12 Next, Arphaxad lived for thirty-five years, and then he conceived Shelah.
Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
13 And after he conceived Shelah, Arphaxad lived for three hundred and three years, and he conceived sons and daughters.
Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
14 Likewise, Shelah lived for thirty years, and then he conceived Eber.
Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
15 And after he conceived Eber, Shelah lived for four hundred and three years, and he conceived sons and daughters.
Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
16 Then Eber lived for thirty-four years, and he conceived Peleg.
Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
17 And after he conceived Peleg, Eber lived for four hundred and thirty years, and he conceived sons and daughters.
Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
18 Likewise, Peleg lived for thirty years, and then he conceived Reu.
Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
19 And after he conceived Reu, Peleg lived for two hundred and nine years, and he conceived sons and daughters.
Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
20 Then Reu lived for thirty-two years, and then he conceived Serug.
Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
21 Likewise, after he conceived Serug, Reu lived for two hundred and seven years, and he conceived sons and daughters.
Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
22 In truth, Serug lived for thirty years, and then he conceived Nahor.
Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
23 And after he conceived Nahor, Serug lived for two hundred years, and he conceived sons and daughters.
Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
24 And so Nahor lived for twenty-nine years, and then he conceived Terah.
Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
25 And after he conceived Terah, Nahor lived for one hundred and nineteen years, and he conceived sons and daughters.
Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
26 And Terah lived for seventy years, and then he conceived Abram, and Nahor, and Haran.
Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
27 And these are the generations of Terah. Terah conceived Abram, Nahor, and Haran. Next Haran conceived Lot.
Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
28 And Haran died before his father Terah, in the land of his nativity, in Ur of the Chaldeans.
Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
29 Then Abram and Nahor took wives. The name of Abram’s wife was Sarai. And the name of Nahor’s wife was Milcah, the daughter of Haran, the father of Milcah, and the father of Iscah.
Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
30 But Sarai was barren and had no children.
Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
31 And so Terah took his son Abram, and his grandson Lot, the son of Haran, and his daughter-in-law Sarai, the wife of his son Abram, and he led them away from Ur of the Chaldeans, to go into the land of Canaan. And they approached as far as Haran, and they dwelt there.
Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
32 And the days of Terah that passed were two hundred and five years, and then he died in Haran.
Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.

< Genesis 11 >