< Ezra 7 >

1 Now after these things, during the reign of Artaxerxes, the king of the Persians, Ezra, the son of Seraiah, the son of Azariah, the son of Hilkiah,
Bayan waɗannan abubuwa, a zamanin Artazerzes sarkin Farisa, sai Ezra ɗan Serahiya, ɗan Azariya, ɗan Hilkiya,
2 the son of Shallum, the son of Zadok, the son of Ahitub,
ɗan Shallum, ɗan Zadok, ɗan Ahitub,
3 the son of Amariah, the son of Azariah, the son of Meraioth,
ɗan Amariya, ɗan Azariya, ɗan Merahiyot,
4 the son of Zerahiah, the son of Uzzi, the son of Bukki,
ɗan Zerahiya, ɗan Uzzi, ɗan Bukki,
5 the son of Abishua, the son of Phinehas, the son of Eleazar, the son of Aaron, priest from the beginning,
ɗan Abishuwa, ɗan Finehas, ɗan Eleyazar, ɗan Haruna babban firist.
6 this same Ezra, ascended from Babylon; and he was a proficient scribe in the law of Moses, which the Lord God gave to Israel. And the king granted to him his every petition. For the hand of the Lord, his God, was over him.
Shi Ezra ɗin ya zo daga Babilon. Shi malami ne ya kuma san Dokar Musa sosai wadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya bayar. Sarki ya ba shi duk abin da ya roƙa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
7 And some from the sons of Israel, and from the sons of the priests, and from the sons of the Levites, and from the singing men, and from the gatekeepers, and from the temple servants ascended to Jerusalem, in the seventh year of king Artaxerxes.
Waɗansu Isra’ilawa, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da masu aiki a haikali su ma suka zo Urushalima a shekara ta bakwai a zamanin mulkin sarki Artazerzes.
8 And they arrived at Jerusalem in the fifth month, in the same seventh year of the king.
Ezra ya iso Urushalima a wata na biyar na shekara ta bakwai na kama mulkin sarkin.
9 For on the first day of the first month, he began to ascend from Babylon, and on the first day of the fifth month, he arrived at Jerusalem. For the good hand of his God was over him.
Ya fara tafiyarsa daga Babilon a rana ta farko ga watan farko, ya kuma iso Urushalima a rana ta farko ga watan biyar, gama alherin Allahnsa yana tare da shi.
10 For Ezra prepared his heart, so that he might search the law of the Lord, and so that he might keep and teach precept and judgment in Israel.
Gama Ezra ya miƙa kansa ga bincike da kuma kiyaye Dokar Ubangiji, da kuma koya wa Isra’ilawa dokoki da kuma umarnan Ubangiji.
11 Now this is a copy of the letter of the edict, which king Artaxerxes gave to Ezra, the priest, a scribe well-taught in the words and precepts of the Lord and in his ceremonies in Israel:
Ga wasiƙar da sarki Artazerzes ya ba Ezra wanda yake firist da kuma malami, mutumin da yake cike da sani game da dokoki da kuma umarnan Ubangiji wa Isra’ila.
12 “Artaxerxes, king of kings, to Ezra, the priest, a very learned scribe of the law of the God of heaven: a greeting.
Artazerzes, sarkin sarakuna. Zuwa ga Ezra firist, malamin Dokar Allah na sama. Gaisuwa.
13 It has been decreed by me, that whosoever wishes, among the people of Israel and their priests and Levites within my kingdom, to go to Jerusalem, may go with you.
Yanzu ina ba da umarni cewa duk wani mutumin Isra’ilan da yake cikin mulkina, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da suke so su tafi tare da kai zuwa Urushalima za su iya tafiya.
14 For you have been sent from the face of the king and his seven counselors, so that you may visit Judea and Jerusalem by the law of your God, which is in your hand,
Sarki ne da mashawartansa guda bakwai suka aike ka don ka je ka ga halin da Yahuda da Urushalima suke ciki game da dokokin Allahnka, waɗanda suke a hannunka.
15 and so that you may carry the silver and gold, which the king and his counselors have freely offered to the God of Israel, whose tabernacle is in Jerusalem.
Za ka kuma tafi da zinariya da azurfa waɗanda sarki da mashawartansa suka ba da kyautar yardar rai ga Allah na Isra’ila, wanda haikalinsa ke a Urushalima,
16 And all the silver and gold, as much as you will find in the entire province of Babylon, and which the people will wish to offer, and which some of the priests will offer freely to the house of their God, which is in Jerusalem,
haɗe da duk zinariya da azurfan da za ka iya samu a Babilon, da kuma duk bayarwar yardar rai daga mutane da firistoci, domin haikalin Allahnsu da yake a Urushalima.
17 accept it freely. And with this money, carefully purchase calves, rams, lambs, and their sacrifices and libations, and offer these upon the altar of the temple of your God, which is in Jerusalem.
Ka tabbata ka yi amfani da kuɗin nan don ka sayi bijimai, da raguna, da’yan raguna, da hadayu na gari, da na sha, ka kuma miƙa su a kan bagade na haikalin Allahnka a Urushalima.
18 But also, whatever it will please you and your brothers to do with the remainder of the silver and gold, do so in accord with the will of your God.
Sa’an nan kai da’yan’uwanka Yahudawa ku yi abin da kuka ga ya fi kyau da sauran zinariya da azurfa ɗin bisa ga nufin Allah.
19 Likewise, the vessels that have been given to you for the ministry of the house of your God, deliver these to the sight of God in Jerusalem.
Ka kai wa Allah na Urushalima duk kayan da aka ba ka amanarsu don yin sujada a haikalin Allahnka.
20 Then, whatever more will be needed for the house of your God, as much as is necessary for you to spend, it shall be given from the treasury, and from the king’s finances,
Duk kuma wani abin da ake bukata domin haikalin Allahnka, daga ɗakunan ajiya sarki za ka fitar da kuɗin.
21 and by me. I, king Artaxerxes, have appointed and decreed to all the keepers of the public treasury, those who are beyond the river, that whatever Ezra, the priest, a scribe of the law of the God of heaven, shall ask of you, you shall provide it without delay,
Yanzu fa ni, Sarki Artazerzes, ina ba da umarni ga kowane ma’aji na Kewayen Kogin Yuferites su tanada duk abin da Ezra firist, wanda kuma yake malamin Dokar Allah na sama zai bukaci,
22 even up to one hundred talents of silver, and up to one hundred cors of wheat, and up to one hundred baths of wine, and up to one hundred baths of oil, and truly salt without measure.
har zuwa talenti ɗari na azurfa, da mudu ɗari na alkama, da garwa ɗari na ruwan inabi, da garwa ɗari na man zaitun, da kuma gishiri ba iyaka.
23 All that pertains to the rite of the God of heaven, let it be distributed scrupulously to the house of the God of heaven, lest perhaps he may become angry against the kingdom of the king and his sons.
A yi duk abin da Allah na sama ya ce don haikalin Allah na sama, sai a yi shi da himma. Me zai sa a jawo wa sarki da’ya’yansa fushin Allah?
24 Likewise, we would make known to you, about all the priests, and the Levites, and the singers, and the gatekeepers, and the temple servants, and the ministers of the house of this God, that you have no authority to impose tax, or tribute, or duty upon them.
Ku kuma san cewa, ba ku da ikon sa firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofin haikali, da masu aiki a gidan Allah, ko waɗansu masu aiki a haikali su biya haraji, ko kuɗin shiga.
25 But as for you, Ezra, in accord with the wisdom of your God, which is in your hand, appoint judges and magistrates, so that they may judge the entire people, which is beyond the river, especially so that they may know the law of your God, but also so as to teach the ignorant freely.
Kai kuma Ezra, bisa ga hikimar da Allah ya ba ka, sai ka zaɓi mahukunta da alƙalai waɗanda za su zama masu yanke hukunci ga dukan mutanen Kewayen Kogin Yuferites, duk waɗanda suka san dokokin Allahnka, ka kuma koya wa duk waɗanda ba su san dokokin ba.
26 And anyone who will not diligently keep the law of your God, and the law of the king, judgment shall be upon him, either to death, or to exile, or to the confiscation of his goods, or certainly to prison.”
Ba shakka duk wanda bai yi biyayya da dokokin Allahnka ba, da kuma dokokin sarki ba dole a yanke masa hukuncin kisa, ko hukuncin kora, ko hukuncin raba shi da mallakarsa, ko kuma hukuncin kulle shi a kurkuku.
27 Blessed be the Lord, the God of our fathers, who has put this into the heart of the king, so that he may glorify the house of the Lord, which is in Jerusalem.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na kakanninmu, ya taɓa zuciyar sarki don yă kawo ɗaukaka ga haikalin Allah a Urushalima ta wannan hanya.
28 For he has turned his mercy toward me in the sight of the king, and his counselors, and all the powerful leaders of the king. And so, having been strengthened by the hand of the Lord, my God, which was upon me, I gathered together some of the leaders of Israel, those who were to go up with me.
Wanda kuma ya sa na sami tagomashi a gaban sarki da mashawartansa, da kuma duk manyan masu muƙami nasa. Gama Ubangiji Allahna yana tare da ni, sai na sami ƙarfin hali na tattara shugabannin mutane daga Isra’ila, don mu tafi tare.

< Ezra 7 >