< Ezra 1 >

1 In the first year of Cyrus, king of the Persians, the Lord stirred up the spirit of Cyrus, king of the Persians, so that the word of the Lord from the mouth of Jeremiah would be fulfilled. And he sent out a voice, throughout his entire kingdom, and also in writing, saying:
A shekara ta farko ta mulkin sarkin Farisa, wato, sarki Sairus, domin a cika maganar Ubangiji da aka yi ta bakin Irmiya, sai Ubangiji ya taɓa zuciyar Sairus sarkin Farisa ya yi shela a duk fāɗin ƙasarsa, ya kuma rubuta cewa,
2 “Thus says Cyrus, the king of the Persians: The Lord, the God of heaven, has given all the kingdoms of the earth to me, and he himself has instructed me that I should build a house for him in Jerusalem, which is in Judea.
“Ga abin da Sairus sarkin Farisa yake shela, “‘Ubangiji Allah na sama ya ba ni iko in yi mulkin duniya duka, ya kuma zaɓe ni in gina masa haikali a Urushalima cikin Yahuda.
3 Who among you is from his entire people? May his God be with him. Let him ascend to Jerusalem, which is in Judea, and let him build the house of the Lord, the God of Israel. He is the God who is in Jerusalem.
Duk wanda yake nasa a cikinku bari Allahnsa yă kasance tare da shi, bari yă tafi Urushalima cikin Yahuda yă gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila, Allah wanda yake a Urushalima.
4 And let all who remain, in all the places wherever they may live, assist him, each man from his place, with silver and gold, and goods and cattle, in addition to whatever they may offer voluntarily to the temple of God, which is in Jerusalem.”
Duk inda akwai mutumin Yahuda da ya rage, sai mutanen da suke zama kusa da shi, su taimake shi da azurfa, da zinariya, da kaya, da kuma dabbobi, tare da kyautai na yardar rai saboda Gidan Allah wanda yake a Urushalima.’”
5 And the leaders of the fathers from Judah and from Benjamin, with the priests, and the Levites, and all those whose spirit was stirred by God, rose up, so that they might ascend to build the temple of the Lord, which was in Jerusalem.
Sai shugabannin zuriyar Yahuda da na Benyamin, da firistoci da Lawiyawa, duk wanda Allah ya taɓa zuciyarsa, suka shirya don su je su gina haikalin Ubangiji a Urushalima.
6 And all those who were all around assisted their hands with vessels of silver and gold, with goods and cattle, with equipment, in addition to whatever they had offered freely.
Dukan maƙwabtansu kuwa suka taimake su da gudummawa na kayan azurfa da na zinariya, da kaya, da dabbobi, da kuma kyautai masu daraja bisa bayarwar yardar rai da suka yi.
7 Likewise, king Cyrus offered the vessels of the temple of the Lord, which Nebuchadnezzar had taken from Jerusalem and had placed in the temple of his god.
Sai sarki Sairus ya fitar da kayan da suke na haikalin Ubangiji waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga Urushalima ya sa a haikalin allahnsa.
8 Now Cyrus, king of Persia, offered these by the hand of Mithredath, the son of the treasurer, and he counted these out to Sheshbazzar, the leader of Judah.
Sairus sarkin Farisa ya sa Mitredat ma’aji ya ƙirga su a gaban Sheshbazzar ɗan sarkin Yahuda.
9 And this is their number: thirty gold bowls, one thousand silver bowls, twenty-nine knives, thirty gold cups,
Ga lissafin kayan. Manyan kwanonin zinariya guda 30 Manyan kwanonin azurfa guda 1,000 Wuƙaƙe guda 29
10 four hundred ten of a second kind of silver cup, one thousand other vessels.
Waɗansu kwanonin zinariya guda 30 Waɗansu kwanonin azurfa guda 410 da waɗansu kayayyaki guda 1,000
11 All the vessels of gold and silver were five thousand four hundred. Sheshbazzar brought all these, with those who ascended from the transmigration of Babylon, into Jerusalem.
Dukan kayayyakin zinariya da na azurfa sun kai 5,400. Sheshbazzar ya kawo kayayyakin nan duka tare da shi lokacin da kamammun suka hauro daga Babilon zuwa Urushalima.

< Ezra 1 >