< Ezekiel 44 >

1 And he turned me back, toward the way of the gate of the outer sanctuary, which looked toward the east. And it was closed.
Sai mutumin ya komo da ni zuwa ƙofar waje na wuri mai tsarki, wadda take fuskantar gabas, tana kuwa a rufe.
2 And the Lord said to me: “This gate will be closed; it will not be opened. And man shall not cross through it. For the Lord, the God of Israel, has entered through it, and it shall be closed
Ubangiji ya ce mini, “Wannan ƙofar za tă kasance a rufe. Ba za a buɗe ta ba; ba wanda zai shiga ta wurinta. Za tă kasance a rufe domin Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya shiga ta wurinta.
3 to the prince. The prince himself will sit at it, so that he may eat bread before the Lord; he will enter by the way of the vestibule of the gate, and he will depart by the same way.”
Sarki kansa ne kaɗai zai zauna a hanyar shiga don yă ci a gaban Ubangiji. Zai shiga ta hanyar shirayin hanyar shiga yă kuma fita a wannan hanya.”
4 And he led me in, along the way of the north gate, in the sight of the house. And I saw, and behold, the glory of the Lord filled the house of the Lord. And I fell upon my face.
Sa’an nan mutumin ya kawo ni ta hanyar ƙofar arewa zuwa gaban haikali. Na duba na kuma ga ɗaukakar Ubangiji tana cika haikalin Ubangiji, sai na fāɗi rubda ciki.
5 And the Lord said to me: “Son of man, set within your heart, and see with your eyes, and hear with your ears all that I am speaking to you about all the ceremonies of the house of the Lord and about all its laws. And set your heart upon the ways of the temple, along all the exits of the sanctuary.
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, ka lura sosai, ka saurara sosai ka kuma mai da hankali ga kome da na faɗa maka game da dukan ƙa’idodi game da haikalin Ubangiji. Ka lura sosai da ƙofar shigar haikali da kuma dukan ƙofofin wuri mai tsarki.
6 And you shall say to the house of Israel, which provokes me: Thus says the Lord God: Let all your wicked deeds be sufficient for you, O house of Israel.
Faɗa wa’yan tawayen gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ayyukan banƙyamarku sun isa haka, ya gidan Isra’ila!
7 For you bring in foreign sons, uncircumcised in heart and uncircumcised in flesh, so that they may be in my sanctuary and may defile my house. And you offer my bread, the fat, and the blood, yet you have broken my covenant by all your wicked deeds.
Ban da dukan sauran ayyukanku na banƙyama, kun kawo baƙi marasa kaciya a zuciya da jiki a wurina mai tsarki, kun kuma ƙazantar da haikalina yayinda kuke miƙa mini abinci, kitse da kuma jini, kun kuma karya alkawarina.
8 And you have not observed the precepts of my sanctuary, yet you have stationed observers of my vigil in my sanctuary for yourselves.
A maimakon yin ayyukanku bisa ga abubuwana masu tsarki, kun sa waɗansu su lura da wurina mai tsarki.
9 Thus says the Lord God: Any foreigner, any foreign son who is in the midst of the sons of Israel, who is uncircumcised in heart and uncircumcised in flesh, shall not enter into my sanctuary.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba baƙo marar kaciya a zuciya da jiki da zai shiga wurina mai tsarki, kai, har ma da baƙin da suke zama a cikin Isra’ila.
10 And as for the Levites, they have withdrawn far away from me, in the errors of the sons of Israel, and they have gone astray from me after their idols, and they have borne their iniquity.
“‘Lawiyawan da suka yi nesa da ni sa’ad da Isra’ila suka kauce da kuma waɗanda suka karkata daga gare ni suka bi gumakansu, dole su ɗauki alhakin zunubinsu.
11 They will be caretakers in my sanctuary, and doorkeepers at the gates of the house, and ministers to the house. They will slay the holocausts and the victims of the people. And they will stand before them, so that they may minister to them.
Za su iya yin hidima a wurina mai tsarki, suna lura da ƙofofin haikali suna kuma hidima a cikinsu; za su iya yankan hadayun ƙonawa da sadaka don mutane su kuma tsaya a gaban mutane su yi musu hidima.
12 But because they ministered to them in the sight their idols, and they became a stumbling block of iniquity to the house of Israel, for this reason, I have lifted up my hand against them, says the Lord God, and they will bear their iniquity.
Amma domin sun yi musu hidima a gaban gumakansu suka sa gidan Isra’ila ya yi zunubi, saboda haka na ɗaga hannu na rantse cewa dole su ɗauki alhakin zunubinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 And they shall not draw near to me, so as to exercise the priesthood for me, and they shall not approach to any of my holy things, which are near the Holy of Holies. Instead, they will bear their shame and their wicked deeds, which they committed.
Ba za su yi kusa don su yi hidima kamar firistoci ko su zo kusa da abubuwana masu tsarki ko hadayuna mafi tsarki ba; dole su sha kunya saboda ayyukansu na banƙyama.
14 And I will make them doorkeepers of the house, for all its ministries and for all that will be done within it.
Duk da haka zan sa su su lura da ayyukan haikali da kuma dukan ayyukan da za a yi a cikinsa.
15 But the priests and the Levites who are the sons of Zadok, who observed the ceremonies of my sanctuary when the sons of Israel went astray from me, these shall draw near to me, so that they may minister for me. And they shall stand in my sight, so that they may offer to me the fat and the blood, says the Lord God.
“‘Amma firistoci, waɗanda suke Lawiyawa kuma zuriyar Zadok waɗanda suka yi aminci ta wurin yin ayyukansu a wurina mai tsarki sa’ad da Isra’ilawa suka kauce daga gare ni, su ne za su zo kusa don hidima a gabana; za su tsaya a gabana don miƙa hadayun kitse da jini, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
16 They shall enter into my sanctuary, and they shall draw near to my table, so that they may minister for me, and so that they may observe my ceremonies.
Su ne kaɗai za su shiga wurina mai tsarki; su ne kaɗai za su zo kusa da teburina don yin hidima a gabana su kuma yi hidimata.
17 And when they enter the gates of the inner court, they shall be clothed with linen garments. Neither shall anything woolen be placed over them, when they minister within the gates of the inner and the outer court.
“‘Sa’ad da suka shiga ƙofofin fili na can ciki, dole su sa tufafin lilin; kada su sa wani rigar da aka yi da ulu yayinda suke hidima a ƙofofin fili na can ciki da cikin haikali.
18 They shall have linen bands on their heads, and linen undergarments over their loins, and they shall not be girded so as to sweat.
Za su naɗa rawunan lilin a kawunansu, su kuma sa wandunan lilin. Kada su sa wani abin da zai sa su yi zuffa.
19 And when they go forth to the outer court to the people, they shall strip off their vestments, in which they ministered, and they shall place them in the storeroom of the sanctuary, and they shall clothe themselves with other garments. And they shall not sanctify the people in their vestments.
Sa’ad da suka fita daga haikali zuwa fili na waje inda mutane suke, sai su tuɓe rigunan da suka yi hidima da su su bar su a tsarkakan ɗakuna, su sa waɗansu riguna, don kada su tsarkake mutane ta wurin rigunansu.
20 Now they shall not shave their heads, and they shall not grow long hair. Instead, they shall trim the hair of their heads.
“‘Ba za su aske kawunansu ko su bar gashin kansu ya yi tsayi ba, amma sai su sausaye gashin kansu.
21 And no priest shall drink wine, when he will be entering into the inner court.
Kada firist ya sha ruwan inabi sa’ad da zai shiga fili na can ciki.
22 And they shall not take as wife a widow or one who has been divorced. Instead, they shall take virgins from the offspring of the house of Israel. But they may also take a widow, if she is the widow of a priest.
Kada su auri gwauruwa ko macen da aka sāke; za su auri budurwai ne kaɗai na Isra’ilawa ko gwaurayen firistoci.
23 And they shall teach my people the difference between holy and defiled, and they shall distinguish for them between clean and unclean.
Za su koyar da mutanena bambanci tsakanin tsarki da rashin tsarki su kuma nuna musu yadda za su bambanta marar tsarki da mai tsarki.
24 And when there has been a controversy, they shall stand in my judgments, and they shall judge. They shall observe my laws and my precepts, in all my solemnities, and they shall sanctify my Sabbaths.
“‘A duk wani rashin jituwa, firistoci za su zama alƙalai su kuma yanke magana bisa ga farillaina. Za su kiyaye dokokina da ƙa’idodina a dukan ƙayyadaddun bukukkuwana, su kuma kiyaye Asabbataina da tsarki.
25 And they shall not enter to a dead person, lest they be defiled, except to father or mother, or son or daughter, or brother, or to a sister who does not have another man. By these, they may become unclean.
“‘Firist ba zai ƙazantar da kansa ta wurin zuwa kusa da gawa ba; amma, in gawar mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ko ɗansa ko’yarsa, ko ɗan’uwansa ko’yar’uwarsa ce, to, ba zai ƙazantar da kansa ba.
26 And after he will have been cleansed, they shall number for him seven days.
Bayan ya tsarkaka, dole yă jira har kwana bakwai.
27 And on the day when he enters into the sanctuary, to the inner court, so that he may minister to me in the sanctuary, he shall make an offering because of his offense, says the Lord God.
A ranar da ya shiga fili na can ciki na wuri mai tsarki don hidima a wuri mai tsarki, zai miƙa hadaya don zunubi saboda kansa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
28 And there shall be no inheritance for them. I am their inheritance. And you shall not give them any possession in Israel. For I am their possession.
“‘Ni ne kaɗai zan zama abin gādon da firistoci za su kasance da shi. Kada ka ba su wani mallaka a Isra’ila; zan zama mallakarsu.
29 They shall eat the victim both for sin and for offenses. And every vowed offering in Israel shall be theirs.
Za su ci hadaya ta gari, hadaya don zunubi da hadaya don laifi; da kuma kowane keɓaɓɓen abu a Isra’ila da za a ba wa Ubangiji zai zama nasu.
30 And the first-fruits of all the firstborn, and all the libations out of all that is offered, shall belong to the priests. And you shall give the first-fruits of your foods to the priest, so that he may return a blessing to your house.
Mafi kyau na nunan farinku da kuma dukan kyautanku na musamman za su zama na firistoci. Za ku ba su rabo na fari na ɓarzajjen hatsinku saboda albarka ta kasance a gidanku.
31 The priests shall not consume anything which has died on its own, or which was seized by a beast, whether from the fowl or the cattle.”
Firistoci ba za su ci mushen tsuntsu ko na dabba ba, ba kuwa za su ci waɗanda namun jeji suka kashe ba.

< Ezekiel 44 >