< Ezekiel 43 >

1 And he led me to the gate which looked toward the way of the east.
Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da take fuskantar gabas,
2 And behold, the glory of the God of Israel entered along the way of the east. And his voice was like the voice of many waters. And the earth was resplendent before his majesty.
sai na ga ɗaukakar Allah na Isra’ila tana tahowa daga gabas. Muryarsa ta yi kamar rurin ruwaye masu gudu, ƙasa kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.
3 And I saw a vision in accord with the form that I had seen when he arrived so that he might destroy the city. And the form was in accord with the sight that I had seen beside the river Chebar. And I fell upon my face.
Wahayin da na gani ya yi kamar wahayin da na gani sa’ad da ya zo don yă hallaka birnin, kamar kuma wahayin da na gani kusa da Kogin Kebar, na kuwa fāɗi rubda ciki.
4 And the majesty of the Lord advanced into the temple, along the way of the gate which looked toward the east.
Ɗaukakar Ubangiji ta shiga haikali ta ƙofar da take fuskantar gabas.
5 And the Spirit lifted me up and brought me into the inner court. And behold, the house was filled with the glory of the Lord.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin fili na can ciki, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
6 And I heard someone speaking to me from the house, and the man who was standing beside me
Yayinda mutumin yana tsaye kusa da ni, na ji wani yana magana da ni daga cikin haikalin.
7 said to me: “Son of man, the place of my throne, and the place of the steps of my feet, is where I live: in the midst of the sons of Israel forever. And the house of Israel, they and their kings, shall no longer defile my holy name by their fornications, and by the ruinous ways of their kings, and by exalted places.
Ya ce, “Ɗan mutum, wannan shi ne kursiyina da wurin tafin ƙafafuna. A nan ne zan zauna a cikin Isra’ilawa har abada. Gidan Isra’ila ba zai ƙara ɓata sunana mai tsarki ba, ko su ko sarakunansu, ta wurin karuwanci da gumakan da ba su da rai, sarakunansu a masujadan kan tudu.
8 They have fabricated their threshold beside my threshold, and their doorposts beside my doorposts. And there was a wall between me and them. And they defiled my holy name by the abominations which they committed. Because of this, I consumed them in my wrath.
Sa’ad da suka sa madogarar ƙofarsu kusa da madogarar ƙofata, da katanga kawai a tsakanina da su, sun ɓata sunana mai tsarki ta wurin ayyukansu masu banƙyama. Saboda haka na hallaka su cikin fushina.
9 Now therefore, let them drive away their fornications, and the ruinous ways of their kings, from before me. And I will live in their midst forever.
Yanzu bari su kawar da karuwancinsu da gumakansu waɗanda ba su da rai na sarakunansu daga gabana, zan kuwa zauna a cikinsu har abada.
10 But as for you, son of man, reveal the temple to the house of Israel, and let them be confounded by their iniquities, and let them measure the fabrication,
“Ɗan mutum, ka bayyana haikalin ga mutanen Isra’ila, don su ji kunya saboda zunubansu. Bari su yi la’akari da fasalin,
11 and let them be ashamed at all the things that they have done. Reveal to them the form and the fabrication of the house, its exits and entrances, and its entire description, and all of its precepts, and its entire order, and all of its laws. And you shall write in their sight, so that they may observe its entire description and its precepts, and so that they may accomplish them.”
kuma in suka ji kunyar abubuwan da suka aikata, sai ka sanar musu fasalin haikalin da shirye-shiryensa, ƙofofinsa na shiga da fita, dukan fasalinsa da dukan ƙa’idodinsa da dokokinsa. Ka rubuta waɗannan a gabansu saboda su yi aminci da fasalinsa su kuma kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
12 This is the law of the house at the summit of the mountain, with all its parts all around. It is the Holy of Holies. Therefore, this is the law of the house.
“Wannan ita ce dokar haikalin. Dukan filin da yake kewaye a kan dutsen, zai zama wuri mafi tsarki. Dokar haikalin ke nan.
13 Now these are the measures of the altar by the most true cubit, which has a cubit and a palm. Its bend was a cubit, and it was a cubit in width. And its boundary, even to its edge and all around, was the width of one palm. The trough of the altar was like this also.
“Waɗannan su ne aune-aunen bagade a tsawon kamu, wannan kamu shi ne kamun tafin hannu. Zurfin magudanar ruwansa kamu ɗaya ne fāɗinsa kuma kamu ɗaya, tare da da’ira kamun tafi ɗaya kewaye da gefensa. Wannan kuma shi ne tsayin bagaden.
14 And from the bend at the floor even to the furthest rim was two cubits, and the width was one cubit. And from the lesser rim even to the greater rim was four cubits, and the width was one cubit.
Daga lambatun da yake a ƙasa har zuwa ƙaramin mahaɗin da yake ƙasa wanda ya kewaye bagade, tsayinsa kamu biyu ne, fāɗinsa kuma kamu guda. Daga ƙaramin mahaɗi zuwa babban mahaɗin wanda ya kewaye bagade, zai zama kamu huɗu, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya.
15 Now the hearth itself was four cubits. And from the hearth going upward, there were four horns.
Murhun bagaden kamu huɗu ne, akwai ƙahoni guda huɗu sun miƙe sama daga murhun.
16 And the hearth was twelve cubits in length by twelve cubits in width, foursquare, with equal sides.
Murhun bagaden murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha biyu, fāɗinsa kuma kamu goma sha biyu.
17 And the rim was fourteen cubits in length, by fourteen cubits in width, at its four corners. And the crown all around it was one half cubit, and its bend was one cubit all around. And its steps turned toward the east.
Gefen bisa ma murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha huɗu fāɗinsa kuma kamu goma huɗu, da da’ira da yake da fāɗin rabin kamu da magudanan ruwa kamu guda kewaye. Matakan bagaden suna fuskantar gabas.”
18 And he said to me: “Son of man, thus says the Lord God: These are the rituals of the altar, in whatever day it will be made, so that holocausts may be offered upon it, and blood may be poured out.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa waɗannan su ne za su zama ƙa’idodi don yin hadaya ta ƙonawa da yayyafawar jini a kan bagaden sa’ad da aka gina shi.
19 And you shall present these to the priests and to the Levites, who are of the offspring of Zadok, those who draw near to me, says the Lord God, so that they may offer to me a calf from the herd on behalf of sin.
Za ka ba da ɗan bijimi a matsayin hadaya ta ƙonawa ga firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, na iyalin Zadok, waɗanda suke zuwa kusa don hidima a gabana, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 And you shall take from its blood, and you shall place it on its four horns, and on the four corners of the rim, and on the crown all around. And so shall you cleanse and expiate it.
Za ka ɗibi jininsa ka zuba shi a ƙahoni huɗu na bagaden a gefen bisa da kuma kewaye da da’irar, ta haka za ka tsarkake bagaden ka kuma yi kafara dominsa.
21 And you shall take the calf, which will be offered for sin, and you shall burn it in a separate place in the house, outside of the sanctuary.
Za ka ɗauki bijimi na hadaya don zunubi ka ƙone shi a sashen da aka shirya na haikalin a wani wuri waje da wuri mai tsarki.
22 And on the second day, you shall offer an immaculate he-goat from among the she-goats on behalf of sin. And they shall expiate the altar, just as they expiated it with the calf.
“A rana ta biyu za ka miƙa bunsuru marar lahani domin hadaya don zunubi, za a kuma tsarkake bagaden yadda aka yi da bijimin.
23 And when you will have completed expiating it, you shall offer an immaculate calf from the herd and an immaculate ram from the flock.
Sa’ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa ɗan bijimi da kuma rago daga cikin garke, dukansu marasa lahani.
24 And you shall offer them in the sight of the Lord. And the priests shall sprinkle salt over them, and they shall offer them as a holocaust to the Lord.
Za ka miƙa su a gaban Ubangiji, firistoci kuma za su barbaɗe gishiri a kansu su kuma miƙa su kamar hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
25 For seven days, you shall offer daily a he-goat on behalf of sin. Also, they shall offer a calf from the herd, and a ram from the flock, ones that are immaculate.
“Kwana bakwai za ka tanada bunsuru kullum domin hadaya don zunubi; za ka kuma tanada ɗan bijimi da rago daga garke, dukansu marasa lahani.
26 For seven days, they shall expiate the altar, and they shall cleanse it, and they shall fill its hand.
Kwana bakwai za su yi kafara saboda bagaden su kuma tsarkake shi; ta haka za su keɓe shi.
27 Then, when the days have been completed, on the eighth day and thereafter, the priests shall offer your holocausts upon the altar along with the peace offering. And I will be pleased with you, says the Lord God.”
A ƙarshen waɗannan kwanaki, daga rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kan bagade. Sa’an nan zan karɓe ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 43 >