< Ezekiel 31 >

1 And it happened that, in the eleventh year, in the third month, on the first of the month, the word of the Lord came to me, saying:
A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na uku a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, speak to Pharaoh, the king of Egypt, and to his people: To whom can you be compared in your greatness?
“Ɗan mutum, faɗa wa Fir’auna sarkin Masar da jama’arsa cewa, “‘Da wa za a kwatanta girmanka?
3 Behold, Assur is like the cedar of Lebanon, with fair branches, and full of leaves, and of high stature, and his summit has been elevated above the thick branches.
Ka dubi Assuriya, ta taɓa zama kamar al’ul a Lebanon da rassa masu kyau suna inuwartar da kurmi; ya yi tsayi ainun kansa ya kai cikin gizagizai.
4 The waters have nourished him. The abyss has exalted him. Its rivers have flowed around his roots, and it has sent forth its streams to all the trees of the regions.
Ruwa ya sa ya yi girma, zurfafan maɓulɓulai sun sa ya yi tsayi; rafuffuka suna gudu kewaye da tushensa yana aika da rafuffukansa zuwa dukan itatuwan kurmi.
5 Because of this, his height was exalted above all the trees of the regions, and his groves were multiplied, and his own branches were elevated, because of the many waters.
Saboda haka ya yi tsayi fiye da sauran itatuwan kurmi; rassansa suka ƙaru suka yi tsayi, suka bazu saboda yalwar ruwaye.
6 And when he had extended his shadow, all the birds of the air made their nests in his branches, and all the beasts of the forest conceived their young under his foliage, and an assembly of the many peoples lived under his shadow.
Dukan tsuntsayen sararin sama suka yi sheƙa a rassansa, dukan namun jeji suka haihu a ƙarƙashin rassansa; dukan al’ummai suka zauna a inuwarsa.
7 And he was most beautiful in his greatness and in the expansion of his groves. For his root was near many waters.
Yana da girma a kyau, da dogayen rassansa da ya baza, gama saiwoyinsa sun nutse can ƙasa har cikin yalwar ruwaye.
8 The cedars in the Paradise of God were not higher than he was. The spruce trees were not equal to his summit, and the plane trees were not equal to his fullness. No tree in the Paradise of God was similar to him or to his beauty.
Al’ul a cikin lambun Allah ba su kai shi ba, balle itatuwan kasharina su kai rassansa, ko itatuwan durumi su kai rassansa, ko itace a lambun Allah ya kai kyansa.
9 For I made him beautiful, and dense with many branches. And all the trees of delight, which were in the Paradise of God, were jealous of him.
Na sa ya yi kyau da yalwar rassa, abin ƙyashi na dukan itatuwan Eden a lambun Allah.
10 Because of this, thus says the Lord God: Since he was sublime in height, and he made his summit green and dense, and his heart was exalted because of his height,
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin ya yi tsayi, kansa kuma ya kai cikin gizagizai, kuma domin ya yi fariya saboda tsayinsa,
11 I have delivered him into the hands of the most powerful one among the Gentiles, so that he will deal with him. I have cast him out, in accord with his impiety.
na miƙa shi ga mai mulkin al’ummai, don yă sāka masa gwargwadon muguntarsa. Na jefar da shi a gefe,
12 And foreigners, and the most cruel among the nations, will cut him down. And they will cast him on the mountains. And his branches will fall in every steep valley, and his grove will be broken apart on every cliff of the earth. And all the peoples of the earth will withdraw from his shadow, and abandon him.
kuma baƙi mafi mugunta na al’ummai suka sare shi suka bar shi. Rassansa sun fāɗi a kan duwatsun da suke cikin dukan kwaruruka; rassansa kuma sun kakkarye, sun fāɗi a cikin dukan magudanan ruwa na ƙasa. Dukan al’umman duniya suka fito daga ƙarƙashin inuwarsa suka bar shi.
13 All the birds of the air lived upon his ruins, and all the beasts of the countryside were among his branches.
Dukan tsuntsaye sararin sama suka zauna a itacen da ya fāɗi, dukan namun jeji kuma suna cikin rassansa.
14 For this reason, none of the trees among the waters will exalt themselves because of their height, nor will they place their summits above the thick branches and foliage, nor will any of those that are irrigated stand out because of their height. For they have all been delivered unto death, to the lowest part of the earth, into the midst of the sons of men, those who descend into the pit.
Saboda haka ba wani daga cikin itatuwan da suke kusa da ruwan da zai taɓa yin fariyar tsawonsa, har kawunansu su kai cikin gizagizai. Ba wani daga cikin itatuwan da ya sha ruwa sosai da zai taɓa yi wannan tsayi; duk an bashe su ga mutuwa, zuwa can ƙasa, a cikin matattu, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
15 Thus says the Lord God: In the day when he descended into hell, I led in grieving. I covered him with the abyss. And I held back its rivers, and I restrained the many waters. Lebanon was saddened over him, and all the trees of the field were struck together. (Sheol h7585)
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da aka yi ƙasa da shi zuwa kabari na rufe zurfafa maɓulɓulai da makoki dominsa; na janye rafuffukansa, aka kuma hana yalwan ruwansa. Saboda shi na rufe Lebanon da baƙin ciki, dukan itatuwan kurmi suka bushe. (Sheol h7585)
16 I shook the Gentiles with the sound of his ruin, when I led him down to hell, with those who were descending into the pit. And all the trees of delights, the finest and best in Lebanon, all that were irrigated with waters, were consoled in the deepest parts of the earth. (Sheol h7585)
Na sa al’ummai suka yi rawar jiki da jin ƙarar fāɗuwarsa sa’ad da na yi ƙasa da shi zuwa kabari tare da waɗanda suka gangara rami. Sai dukan itatuwan Eden, zaɓaɓɓu da kuma mafi kyau na Lebanon, dukan itatuwan da aka yi musu banruwa, sun ta’azantu a ƙarƙashin ƙasa. (Sheol h7585)
17 For they, too, will descend with him into hell, to those who have been slain by the sword. And the arm of each one will reside under his shadow, in the midst of the nations. (Sheol h7585)
Waɗanda suka zauna a inuwarsa, dukan masu tarayyarsa a cikin al’ummai, su ma sun gangara zuwa kabari tare da shi, sun haɗu da waɗanda aka kashe da takobi. (Sheol h7585)
18 To whom can you be compared, O famous and sublime one, among the trees of pleasure? Behold, you have been brought down, with the trees of pleasure, to the lowest part of the earth. You will sleep in the midst of the uncircumcised, with those who have been slain by the sword. This is Pharaoh, and all his multitude, says the Lord God.”
“‘Da wa cikin itatuwan Eden za a kwatanta da kai cikin girma da daraja? Duk da haka kai ma, za a yi ƙasa da kai tare da itatuwan Eden zuwa ƙarƙashin ƙasa; za ka kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi. “‘Fir’auna ke nan da dukan jama’arsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< Ezekiel 31 >