< Ezekiel 23 >

1 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, two women were daughters of one mother,
“Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
3 and they fornicated in Egypt; they committed fornication in their youth. In that place, their breasts were conquered; the breasts of their adolescence were subdued.
Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
4 Now their names were Oholah, the elder, and Oholibah, her younger sister. And I held them, and they bore sons and daughters. As for their names: Oholah is Samaria, and Oholibah is Jerusalem.
Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
5 And then, Oholah committed fornication against me, and she acted madly with her lovers, with the Assyrians who approached her,
“Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
6 who were clothed with hyacinth: rulers and magistrates, passionate youths and all of the horsemen, mounted on horses.
waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
7 And she distributed her fornications to those chosen men, all of them sons of the Assyrians. And she defiled herself with the uncleanness of all those whom she madly desired.
Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
8 Moreover, she also did not abandon her fornications, which she had done in Egypt. For they also slept with her in her youth, and they bruised the breasts of her virginity, and they poured out their fornication upon her.
Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
9 Because of this, I have delivered her into the hands of her lovers, into the hands of the sons of the Assur, whom she has lustfully desired.
“Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
10 They uncovered her shame; they took away her sons and daughters; and they slew her with the sword. And they became infamous women. And they carried out judgments in her.
Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
11 And when her sister, Oholibah, had seen this, she was even more mad with lust than the other. And her fornication was beyond the fornication of her sister.
“Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
12 She shamelessly offered herself to the sons of the Assyrians, to the rulers and magistrates who brought themselves to her clothed with colorful garments, to the horsemen who were carried by horses, and to the youths, all of them exceptional in appearance.
Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
13 And I saw that she had been defiled, and that they both took the same path.
Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
14 And she increased her fornications. And when she had seen men depicted on the wall, the images of the Chaldeans, expressed in colors,
“Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
15 with belts wrapped around the waist, and with dyed headdresses on their heads, having seen the appearance of all the rulers, the likenesses of the sons of Babylon and of the land of the Chaldeans in which they were born,
da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
16 she became mad for them with the desire of her eyes, and she sent messengers to them in Chaldea.
Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
17 And when the sons of Babylon had gone to her, to the bed of breasts, they defiled her with their fornications, and she was polluted by them, and her soul was gorged by them.
Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
18 Also, her fornications were uncovered, and her shame was revealed. And my soul withdrew from her, as my soul had withdrawn from her sister.
Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
19 For she multiplied her fornications, remembering the days of her youth, in which she fornicated in the land of Egypt.
Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
20 And she was mad with lust after lying with them, whose flesh is like the flesh of donkeys, and whose flow is like the flow of horses.
A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
21 And you have revisited the crimes of your youth, when your breasts were conquered in Egypt, and the breasts of your adolescence were subdued.
Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
22 Because of this, Oholibah, thus says the Lord God: Behold, I will raise up against you all of your lovers, with whom your soul has been gorged. And I will gather them together against you all around:
“Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
23 the sons of Babylon, and all the Chaldeans, the nobles, the sovereigns and princes, all the sons of the Assyrians, youths of exceptional form, all the rulers and magistrates, the leaders among leaders, and the renowned riders of horses.
Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
24 And they will overwhelm you, well-equipped with chariot and wheel, a multitude of peoples. They will be armed against you on every side with armor and shield and helmet. And I will give judgment to their eyes, and they will judge you with their judgments.
Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
25 And against you, I will set my zeal, which they will execute upon you with fury. They will cut off your nose and your ears. And what remains will fall by the sword. They will seize your sons and your daughters, and your youngest will be devoured by fire.
Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
26 And they will strip you of your vestments, and take away the articles of your glory.
Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
27 And I will cause your wickedness to cease from you, and your fornication to cease from the land of Egypt. Neither shall you lift up your eyes toward them, and you shall no longer remember Egypt.
Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
28 For thus says the Lord God: Behold, I will deliver you into the hands of those whom you have hated, into the hands by which your soul has been gorged.
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
29 And they will act toward you with hatred, and they will take away all your labors, and they will send you away naked and filled with disgrace. And the shame of your fornication will be revealed: your crimes and your fornications.
Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
30 They have done these things to you, because you have fornicated after the Gentiles, among whom you were defiled by their idols.
sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
31 You have walked in the way of your sister, and so I will give her chalice into your hand.
Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
32 Thus says the Lord God: You will drink the chalice of your sister, deep and wide. You will be held in derision and in ridicule, to a very great extent.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
33 You will be filled with inebriation and sorrow, by the chalice of grief and sadness, by the chalice of your sister Samaria.
Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
34 And you will drink it, and you will empty it, even to the dregs. And you will consume even its particles. And you will wound your own breasts. For I have spoken, says the Lord God.
Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
35 Because of this, thus says the Lord God: Since you have forgotten me, and you have cast me behind your body, so also will you bear your wickedness and your fornications.”
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
36 And the Lord spoke to me, saying: “Son of man, should you not judge Oholah and Oholibah, and announce to them their crimes?
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
37 For they are adulteresses, and blood is in their hands, and they have fornicated with their idols. Moreover, they have offered even their children, whom they bore for me, to them to be devoured.
gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
38 But they have done even this to me: They have defiled my sanctuary on the same day, and they have profaned my Sabbaths.
Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
39 And when they immolated their children to their idols, they also entered my sanctuary on the same day, so that they defiled it. They have done these things, even in the midst of my house.
A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
40 They sent for men who were coming from far away, to whom they had sent a messenger. And so, behold, they arrived, those for whom you washed yourself, and smeared cosmetics around your eyes, and were adorned with feminine ornaments.
“Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
41 You sat upon a very beautiful bed, and a table was adorned before you, on which you placed my incense and my ointment.
Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
42 And the voice of a multitude was exulting within her. And concerning certain men, who were being led out of a multitude of persons, and who were arriving from the desert, they placed bracelets on their hands and beautiful crowns on their heads.
“Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
43 And I said about her, as she was being worn away by her adulteries, ‘Even now, she continues in her fornication!’
Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
44 And they entered to her, as if to a kept woman. So did they enter to Oholah and Oholibah, nefarious women.
Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
45 But there are just men; these shall judge them with the judgment of adulteresses and with the judgment of those who shed blood. For they are adulteresses, and blood is on their hands.
Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
46 For thus says the Lord God: Lead upon them a multitude, and hand them over to tumult and to pillaging.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
47 And may they be stoned with the stones of the peoples, and may they be pierced with their own swords. They will put to death their sons and daughters, and they will burn their houses with fire.
Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
48 And I will take away wickedness from the land. And all women shall learn not to act according to their wickedness.
“Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
49 And they will set your own crimes upon you, and you will bear the sins of your idols. And you shall know that I am the Lord God.”
Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 23 >