< Exodus 4 >

1 Responding, Moses said, “They will not believe me, and they will not listen to my voice, but they will say: ‘The Lord has not appeared to you.’”
Musa ya amsa ya ce, “In ba su gaskata ni ba, suka kuma ce, ‘Ubangiji bai bayyana gare ka ba fa’?”
2 Therefore, he said to him, “What is that you hold in your hand?” He answered, “A staff.”
Sai Ubangiji ya ce, “Mene ne wannan a hannunka?” Musa ya amsa ya ce, “Sanda.”
3 And the Lord said, “Cast it down upon the ground.” He cast it down, and it was turned into a snake, so that Moses fled away.
Sai Ubangiji ya ce, “Jefa shi ƙasa.” Musa ya jefa shi ƙasa, sai sandan ya zama maciji, Musa kuwa ya gudu daga gare shi.
4 And the Lord said, “Reach out your hand, and take hold of its tail.” He reached out his hand and took hold, and it was turned into a staff.
Sai Ubangiji ya ce masa, “Sa hannunka ka ɗauke shi ta wutsiya.” Sai Musa ya miƙa hannu, ya kama macijin, macijin kuwa ya dawo sanda a hannunsa.
5 “So may they believe,” he said, “that the Lord God of their fathers, the God of Abraham, the God of Isaac, and the God of Jacob, has appeared to you.”
Ubangiji ya ce, “Wannan zai sa su ba da gaskiya cewa Ubangiji, Allah na kakanninsu, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da kuma Allah da Yaƙub, ya bayyana gare ka.”
6 And the Lord said again, “Put your hand into your bosom.” And when he had put it into his bosom, he brought it out leprous, resembling snow.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Sa hannunka cikin rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, sa’ad da ya fitar da shi, sai hannun ya a kuturce fari fat, kamar ƙanƙara.
7 “Put your hand back,” he said, “into your bosom.” He put it back and brought it out again, and it was like the rest of his flesh.
Sai Ubangiji ya ce, “Yanzu, mayar da hannunka a rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, da ya fitar da shi, sai hannun ya koma kamar sauran jikinsa.
8 “If they will not believe you,” he said, “and will not listen to the sermon of the first sign, then they will believe the word of the subsequent sign.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “In ba su gaskata ba, ko kuma ba su kula da mu’ujiza ta fari ba, wataƙila su gaskata da ta biyun.
9 But if they will not believe even these two signs, and they will not listen to your voice: take from the water of the river, and pour it upon the dry land, and whatever you will have drawn from the river will be turned into blood.”
Amma in ba su gaskata mu’ujizan nan biyu ba, ko kuwa ba su saurare ka ba, sai ka ɗibo ruwa daga Nilu, ka zuba a busasshiyar ƙasa. Ruwan da ka ɗebo daga kogin zai zama jini a ƙasar.”
10 Moses said: “I beg you, O Lord, I was not eloquent yesterday or the day before. And from the time that you have spoken to your servant, I have a greater impediment and slowness of tongue.”
Musa ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji, ni ban mai iya magana ba ne, ban taɓa iya ba, ko a yanzu ma, bayan ka yi magana da ni, gama ni mai nauyin baki ne, mai nauyin harshe kuma.”
11 The Lord said to him: “Who made the mouth of man? And who has formed the mute and the deaf, the seeing and the blind? Was it not I?
Ubangiji ya ce masa, “Wa ya ba mutum bakinsa? Wa yake maishe shi kurma ko bebe? Wa yake ba shi gani ko yă makanta shi? Ashe ba Ni Ubangiji ba ne?
12 Go on, therefore, and I will be in your mouth. And I will teach you what you shall say.”
Yanzu tafi, zan taimake ka ka yi magana, zan kuma koya maka abin da za ka faɗa.”
13 But he said, “I beg you, O Lord, send whomever else you would send.”
Amma Musa ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, ka nemi wani ka aika.”
14 The Lord, being angry at Moses, said: “Aaron the Levite is your brother. I know that he is eloquent. Behold, he is going out to meet you, and seeing you, he will rejoice in heart.
Sai Ubangiji ya yi fushi da Musa ya ce, “Ɗan’uwanka Haruna Balawe, ba ya nan ne? Na san ya iya magana. Ya riga ya kama hanya don yă sadu da kai, zai kuma yi farin ciki sa’ad da ya gan ka.
15 Speak to him, and put my words in his mouth. And I will be in your mouth and in his mouth, and I will reveal to you what you must do.
Za ka yi masa magana. Ka kuma sa masa maganata a baki; zan kuma taimake ku magana, in koya muku abin da za ku yi.
16 He will speak for you to the people, and he will be your mouth. But you will be with him in those things that pertain to God.
Zai yi magana da mutane a madadinka, zai zama kamar bakinka, kai kuwa kamar Allah a gare shi.
17 Also, take this staff into your hand; with it you will accomplish the signs.”
Amma ka ɗauki wannan sanda a hannunka domin yă aikata mu’ujizan.”
18 Moses went forth, and he returned to Jethro, his father in law, and he said to him, “I shall go and return to my brothers in Egypt, so that I may see if they are still alive.” And Jethro said to him, “Go in peace.”
Sai Musa ya koma wurin Yetro surukinsa, ya ce masa, “Bari in koma wurin mutanena a Masar, in ga ko da mai rai a cikinsu.” Yetro ya ce, “Tafi, ka kuma sauka lafiya.”
19 And so the Lord said to Moses in Midian: “Go, and return to Egypt. For all those who sought your life have died.”
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa a Midiyan, “Koma Masar, domin dukan mutanen da suke neman su kashe ka sun mutu.”
20 Therefore, Moses took his wife and his sons, and he placed them upon a donkey, and he returned into Egypt, carrying the staff of God in his hand.
Sai Musa ya ɗauki matarsa da’ya’yansa maza, ya sa su a kan jaki, suka kama hanya zuwa Masar. Ya kuma ɗauki sandan Allah a hannunsa.
21 And the Lord said to him, as he was returning to Egypt: “See that you accomplish, in the sight of Pharaoh, all the wonders that I have placed in your hand. I will harden his heart, and he will not release the people.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Bayan ka koma Masar, ka tabbata ka aikata dukan mu’ujizan da na sa cikin ikonka a gaban Fir’auna. Amma zan taurare zuciyarsa domin kada yă bar mutanen su tafi.
22 And you shall say to him: ‘Thus says the Lord: Israel is my firstborn son.
Sa’an nan ka gaya wa Fir’auna, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce; Isra’ila shi ne ɗan farina,
23 I have said to you: Release my son, so that he may serve me. And you were not willing to release him. Behold, I will put to death your firstborn son.’”
na gaya maka, “Ka bar ɗana yă tafi domin yă yi mini sujada.” Amma ka ƙi ka bari yă tafi, saboda haka zan kashe ɗan farinka.’”
24 And while he was on the journey, at an inn, the Lord met him, and he was willing to kill him.
Ya zama kuwa sa’ad da Musa yake masauki a kan hanya sai Ubangiji ya gamu da shi, ya nema ya kashe shi.
25 For this reason, Zipporah took a very sharp stone, and she circumcised the foreskin of her son, and she touched his feet, and she said, “You are a bloody spouse to me.”
Amma Ziffora ta ɗauki dutsen ƙanƙara mai ci, ta yanke loɓar ɗanta ta taɓa ƙafafun Musa da shi. Ta ce, “Tabbatacce kai angon jini ne a gare ni.”
26 And he released him, after she had said, “You are a bloody spouse,” because of the circumcision.
Sai Ubangiji ya ƙyale shi. (A lokacin ta ce “angon jini,” tana nufin kaciya.)
27 Then the Lord said to Aaron, “Go into the desert to meet Moses.” And he went directly to meet him on the mountain of God, and he kissed him.
Ubangiji ya ce wa Haruna, “Tafi cikin hamada ka sadu da Musa.” Sai ya sadu da Musa a dutsen Allah, ya sumbace shi.
28 And Moses explained to Aaron all the words of the Lord, by which he had sent him, and the signs which he had commanded.
Sai Musa ya gaya wa Haruna dukan abin da Ubangiji ya aike yă faɗa, da kuma dukan mu’ujizan da ya umarce shi yă aikata.
29 And they arrived at the same time, and they gathered together all the elders of the sons of Israel.
Musa da Haruna suka tattara dukan dattawan Isra’ilawa,
30 And Aaron spoke all the words which the Lord had said to Moses. And he accomplished the signs in the sight of the people,
sai Haruna ya gaya musu dukan abin da Ubangiji ya ce wa Musa. Ya kuma aikata mu’ujizan a gaban mutanen,
31 and the people believed. And they heard that the Lord had visited the sons of Israel, and that he had looked with favor upon their affliction. And falling prostrate, they worshiped.
sai suka gaskata. Sa’ad da suka ji cewa Ubangiji ya damu da su, ya kuma ga azabarsu, sai suka durƙusa suka yi sujada.

< Exodus 4 >