< Exodus 24 >

1 He also said to Moses: “Ascend to the Lord, you and Aaron, Nadab and Abihu, and seventy elders out of Israel, and adore from a distance.
Ana nan sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ku hauro zuwa wurina, kai da Haruna, Nadab da Abihu, da kuma dattawa saba’in a cikin Isra’ila. Za ku yi sujada da ɗan nisa,
2 And only Moses will ascend to the Lord, and these shall not approach. Neither shall the people ascend with him.”
sai Musa kaɗai zai kusaci Ubangiji. Amma sauran kada su zo kusa, kada kuma jama’a su hau tare da shi.”
3 Therefore, Moses went and explained to the people all the words of the Lord, as well as the judgments. And all the people responded with one voice: “We will do all the words of the Lord, which he has spoken.”
Sa’ad da Musa ya tafi ya faɗa wa mutanen duk kalmomin Ubangiji da dokokinsa, sai suka amsa da murya ɗaya suna cewa, “Duk abin da Ubangiji ya faɗa, za mu yi.”
4 Then Moses wrote all the words of the Lord. And rising up in the morning, he built an altar at the base of the mountain, with twelve titles according to the twelve tribes of Israel.
Sai Musa ya rubuta duk abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tashi kashegari da sassafe ya gina bagade kusa da dutsen, ya aza al’amudai goma sha biyu bisa ga kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
5 And he sent youths from the sons of Israel, and they offered holocausts, and they immolated calves as peace-offerings to the Lord.
Sai ya aiki samarin Isra’ilawa, suka miƙa hadaya ta ƙonawa, suka kuma miƙa ƙananan bijimai don hadaya ta salama ga Ubangiji.
6 And so Moses took one half part of the blood, and he put it into bowls. Then the remaining part he poured over the altar.
Musa ya ɗauki rabin jinin ya zuba a cikin kwanoni, rabin kuma ya yayyafa a kan bagaden.
7 And taking up the book of the covenant, he read it in the hearing of the people, who said: “All that the Lord has spoken, we will do, and we will be obedient.”
Sa’an nan ya ɗauki Littafin Alkawari ya karanta wa mutane. Suka amsa suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa; za mu yi biyayya.”
8 In truth, taking up the blood, he sprinkled it on the people, and he said, “This is the blood of the covenant, which the Lord has formed with you concerning all these words.”
Musa ya kuma ɗauki jinin, ya yayyafa a kan mutanen ya ce, “Wannan shi ne jinin alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, bisa ga dukan waɗannan kalmomi.”
9 And Moses and Aaron, Nadab and Abihu, and seventy of the elders of Israel ascended.
Musa da Haruna, Nadab da Abihu, da dattawa saba’in, Allah na Isra’ila suka haura
10 And they saw the God of Israel. And under his feet was something like a work of sapphire stone, or like the sky, when it is serene.
suka kuma ga Allah na Isra’ila. A ƙarƙashin ƙafafunsa akwai wani abu wanda aka yi da saffaya, mai haske kuma kamar sararin sama kansa.
11 Neither did he lay his hand upon those of the sons of Israel who were at a distance. And they saw God, and they ate and drank.
Amma Allah bai yi wa shugabannin Isra’ila wani abu ba; suka ga Allah, suka ci suka kuma sha.
12 Then the Lord said to Moses: “Ascend to me on the mountain, and be there. And I will give to you tablets of stone, and the law and the commandments that I have written. So may you teach them.”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Hauro wurina a kan dutse, ka tsaya a nan, zan ba ka allunan dutsen, da doka da umarnan da na rubuta don koyonsu.”
13 Moses rose up, with Joshua his minister. And Moses, ascending on the mountain of God,
Sa’an nan Musa ya fita tare da Yoshuwa mataimakinsa, ya kuwa hau kan dutsen Allah.
14 said to the elders: “Wait here, until we return to you. You have Aaron and Hur with you. If any question arises, you shall refer it to them.”
Ya ce wa dattawan, “Ku jira mu a nan, sai mun dawo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai yă je wurinsu.”
15 And when Moses had ascended, a cloud covered the mountain.
Da Musa ya hau dutsen, sai girgije ya rufe dutsen,
16 And the glory of the Lord dwelt upon Sinai, covering it with a cloud for six days. And on the seventh day, he called to him from the middle of the mist.
sai ɗaukakar Ubangiji ta sauka a kan Dutsen Sinai, kwana shida girgije ya rufe dutsen, a rana ta bakwai, sai Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.
17 Now the appearance of the glory of the Lord was like a burning fire over the summit of the mountain in the sight of the sons of Israel.
Ga Isra’ilawa dai, ɗaukakar Ubangiji ta yi kamar wuta mai ci a kan dutse.
18 And Moses, entering into the midst of the cloud, ascended the mountain. And he was there for forty days and forty nights.
Sa’an nan Musa ya shiga girgijen ya hau kan dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba’in da dare arba’in.

< Exodus 24 >