< Exodus 19 >

1 In the third month of the departure of Israel from the land of Egypt, in that day, they arrived in the wilderness of Sinai.
A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
2 Thus, setting out from Raphidim, and going directly to the desert of Sinai, they encamped in the same place, and there Israel pitched their tents away from the region of the mountain.
Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
3 Then Moses ascended to God. And the Lord called to him from the mountain, and he said: “This you shall say to the house of Jacob, and announce to the sons of Israel:
Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
4 ‘You have seen what I have done to the Egyptians, in what way I carried you upon the wings of eagles and how I have taken you for myself.
‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
5 If, therefore, you will hear my voice, and you will keep my covenant, you will be to me a particular possession out of all people. For all the earth is mine.
Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
6 And you will be to me a priestly kingdom and a holy nation.’ These are the words that you will speak to the sons of Israel.”
za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
7 Moses went, and calling together those greater by birth among the people, he set forth all the words which the Lord had commanded.
Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
8 And all the people responded together: “Everything that the Lord has spoken, we shall do.” And when Moses had related the words of the people to the Lord,
Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
9 the Lord said to him: “Soon now, I will come to you in the mist of a cloud, so that the people may hear me speaking to you, and so that they may believe you continuously.” Therefore, Moses reported the words of the people to the Lord,
Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
10 who said to him: “Go to the people, and sanctify them today, and tomorrow, and let them wash their garments.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
11 And let them be prepared on the third day. For on the third day, the Lord will descend, in the sight of all the people, over Mount Sinai.
Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
12 And you will establish limits for the people all around, and you will say to them: ‘Take care not to ascend to the mountain, and that you do not touch its parts. All who touch the mountain, shall die a death.’
Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
13 Hands shall not touch him, but he shall be crushed with stones, or he shall be pierced through with darts. Whether it be a beast or a man, he shall not live. For when the trumpet begins to sound, perhaps they might go up toward the mountain.”
Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
14 And Moses came down from the mountain to the people, and he sanctified them. And when they had washed their garments,
Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
15 he said to them, “Be prepared on the third day, and do not draw near to your wives.”
Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
16 And now, the third day arrived and the morning dawned. And behold, thunders began to be heard, and also lightning flashed, and a very dense cloud covered the mountain, and the noise of the trumpet resounded vehemently. And the people who were in the camp were fearful.
A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
17 And when Moses had led them out to meet God, from the place of the camp, they stood at the base of the mountain.
Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
18 Then all of Mount Sinai was smoking. For the Lord had descended over it with fire, and smoke ascended from it, as from a furnace. And the entire mountain was terrible.
Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
19 And the sound of the trumpet gradually increased to be louder, and extended to be longer. Moses was speaking, and God was answering him.
sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
20 And the Lord descended over Mount Sinai, to the very top of the mountain, and he called Moses to its summit. And when he had ascended there,
Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
21 he said to him: “Descend, and call the people to witness, lest they might be willing to transgress the limits, so as to see the Lord, and a very great multitude of them might perish.
sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
22 Likewise, the priests who approach toward the Lord, let them be sanctified, lest he strike them down.”
Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
23 And Moses said to the Lord: “The people are not able to ascend to Mount Sinai. For you testified, and you commanded, saying: ‘Set limits around the mountain, and sanctify it.’”
Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
24 And the Lord said to him, “Go, descend. And you shall ascend, and Aaron with you. But let not the priests or the people transgress the limits, nor ascend to the Lord, lest perhaps he may put them to death.”
Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
25 And Moses descended to the people, and he explained everything to them.
Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.

< Exodus 19 >