< Esther 4 >

1 When Mordecai had heard this, he tore his garments and put on sackcloth, strewing ashes on his head, and he cried out with a loud voice in the main street of the city, revealing the anguish of his soul.
Sa’ad da Mordekai ya sami labari game da dukan abin da aka yi, sai ya yayyage rigunansa, ya sanya tsummokin makoki, ya zuba toka a kā, ya kuma shiga ciki birni yana kuka mai zafi da ƙarfi.
2 And he continued with this lamenting, even up to the gate of the palace, for no one clothed with sackcloth is permitted to enter the king’s court.
Amma ya kai bakin ƙofar sarki ne kawai, gama ba a yarda wani sanye da tsummokin makoki yă shiga cikin birni ba.
3 Likewise, in all provinces, towns, and places where the king’s cruel decision arrived, there was extraordinary mourning among the Jews with fasting, wailing, and weeping, with many using sackcloth and ashes for their bed.
Aka yi makoki sosai da azumi, da kuka mai zafi a cikin Yahudawa a kowane lardin da aka kai doka da kuma umarnin sarki. Mutane da yawa suka kwanta a cikin tsummokin makoki da kuma toka.
4 Then Esther’s maids and eunuchs went in and informed her. When she heard it, she was shocked, and she sent a garment to clothe him and to take away the sackcloth, but he would not accept it.
Sa’ad da bayi da bābānnin Esta suka zo suka faɗa mata game da Mordekai, sai ta damu ƙwarai. Ta aika masa da riguna domin yă sa a maimakon tsummokin makoki, amma ya ƙi.
5 And she sent for Hathach the eunuch, whom the king had appointed to minister to her, and she instructed him to go to Mordecai and to discern from him why he was doing this.
Sai Esta ta kira Hatak, ɗaya daga cikin bābānnin sarkin da aka ba shi aikin lura da ita, ta umarce shi yă yi tambaya me ke damun Mordekai da kuma me ya jawo haka.
6 And departing, Hathach went to Mordecai, who was standing in the street of the city, in front of the palace entrance.
Saboda haka Hatak ya tafi wurin Mordekai a dandalin birni, a gaban ƙofar sarki.
7 He told him everything that had happened, how Haman had promised to transfer silver into the king’s treasury for the death of the Jews.
Mordekai ya faɗa masa duk abin da ya faru da shi, haɗe da yawan kuɗin da Haman ya yi alkawari zai zuba a ma’ajin fada don a hallaka Yahudawa.
8 Also, he gave him a copy of the edict that was hanging up in Susa, so that he would show it to the queen and advise her to go in to the king and beg him on behalf of her people.
Ya kuma ba shi kofi na rubutaccen doka na kakkaɓe su, wanda aka wallafa a Shusha don yă nuna wa Esta, yă bayyana mata. Mordekai ya faɗa wa Hatak yă iza ta tă tafi gaban sarki domin tă yi roƙo don jinƙai, tă kuma roƙe shi saboda mutanenta.
9 And Hathach returned and informed Esther of all that Mordecai had said.
Hatak ya koma ya ba wa Esta rahoton abin da Mordekai ya faɗa.
10 She answered him, and ordered him say to Mordecai:
Sa’an nan Esta ta umarce Hatak yă ce wa Mordekai,
11 “All the servants of the king and all the provinces that are under his realm understand that anyone, whether man or woman, who enters the king’s inner court, who has not been summoned, is immediately to be put to death without any delay, unless the king should happen to extend the golden scepter to him, as a sign of clemency, so that he will be able to live. How then can I go in to the king, when, for thirty days now, I have not been called to him?”
“Dukan hafsoshin sarki da mutanen lardunan sarki sun san cewa duk wanda ya tafi wurin sarki a shirayi na ciki, mace ko namiji, ba tare da an kira shi ba, doka ɗaya ce take kan mutum, wato, kisa. Abu guda kawai da ya sha bamban shi ne sai wanda sarki ya miƙa wa sandan sarauta na zinariya don yă rayu. Kwana talatin ke nan ba a kira ni in tafi wurin sarki ba.”
12 And when Mordecai had heard this, he again sent word to Esther, saying, “Do not think that you will save so much as your own soul, just because you are in the king’s house and are above all the Jews.
Sa’ad da aka kai wa Mordekai rahoton maganan Esta,
13 And when Mordecai had heard this, he again sent word to Esther, saying, “Do not think that you will save so much as your own soul, just because you are in the king’s house and are above all the Jews.
sai ya mayar da wannan amsa wa Esta cewa, “Kada ki yi tsammani cewa don kina a cikin gidan sarki, ke kaɗai cikin dukan Yahudawa za ki tsira.
14 For, if you remain silent now, the Jews will be delivered through some other opportunity, but you and your father’s house will perish. And who knows whether you have come to the kingdom for this reason, so that you would be prepared for such a time as this?”
Gama in kin yi shiru a wannan lokaci, taimako da ceto zai zo daga wani wuri saboda Yahudawa, amma ke da gidanki za ku hallaka. Wa ya san ko saboda irin wannan lokaci ne kika sami wannan muƙami?”
15 And again Esther sent to Mordecai in these words:
Sai Esta ta aika da wannan amsa ga Mordekai cewa,
16 “Go and gather together all the Jews whom you will find in Susa, and pray for me. Neither eat nor drink for three days and three nights, and I will fast with my handmaids similarly, and then I will go in to the king, doing what is against the law, not having been called, and so expose myself to mortal danger.”
“Ka tafi, ka tattara dukan Yahudawan da suke Shusha, ku yi azumi saboda ni. Kada ku ci ko ku sha, dare da rana har kwana uku. Ni kuwa da bayina za mu yi azumi yadda kuke yi. Idan aka yi haka, zan tafi wurin sarki, ko da yake wannan karya doka ce. Idan na hallaka, to, na hallaka.”
17 And so Mordecai went, and he did everything that Esther had instructed him.
Saboda haka, Mordekai ya tafi, ya aikata dukan umarnan Esta.

< Esther 4 >