< Ecclesiastes 5 >

1 Guard your foot, when you step into the house of God, and draw near, so that you may listen. For obedience is much better than the sacrifices of the foolish, who do not know the evil that they are doing.
Ka lura da matakanka sa’ad da ka tafi gidan Allah. Ka je kusa don ka saurara a maimakon miƙa hadaya kamar wawaye, waɗanda ba su san sun yi laifi ba.
2 You should not speak anything rashly, nor should your heart be hasty to present a word before God. For God is in heaven, and you are on earth. For this reason, let your words be few.
Kada ka yi subul da bakinka, kada zuciyarka tă yi garajen furta wani abu a gaban Allah. Allah yana sama kai kuma kana duniya, saboda haka, kada kalmominka su zama da yawa.
3 Dreams follow many worries, and in many words foolishness will be found.
Kamar yadda son cika buri yakan zo sa’ad da kana da yawan damuwa, haka jawabin wawa yake sa’ad da yake yawan magana.
4 If you have vowed anything to God, you should not delay to repay it. And whatever you have vowed, render it. But an unfaithful and foolish promise displeases him.
Sa’ad da ka yi alkawari ga Allah, kada ka ɓata lokaci wajen cika shi. Ba ya jin daɗin wawaye; ka cika alkawarinka.
5 And it is much better not to make a vow, than, after a vow, not to fulfill what was promised.
Gara kada ka yi alkawari, da ka yi amma ba ka cika ba.
6 You should not use your mouth so as to cause your flesh to sin. And you should not say, in the sight of an Angel, “There is no Providence.” For God, being angry at your words, may scatter all the works of your hands.
Kada ka bar bakinka ya kai ga yin zunubi. Kada kuma ka kai ƙara wurin ɗan saƙon haikali cewa, “Alkawarin da na yi kuskure ne.” Me ya sa Allah yake fushi a kan abin da ka faɗa har yă lalatar da aikin hannuwanka?
7 Where there are many dreams, there are many vanities and innumerable words. Yet truly, you must fear God.
Yawan buri da yawan magana ba su da amfani. Saboda haka, ka ji tsoron Allah.
8 If you see false accusations against the indigent, and violent judgments, and subverted justice in the government, do not be surprised over this situation. For those in high places have others who are higher, and there are still others, more eminent, over these.
In ka ga ana zaluntar matalauta a wani yanki, ba a yin adalci, ana kuma tauye hakki, kada ka yi mamakin waɗannan abubuwa; domin akwai wani jami’in da yake bisa da wani, a bisansu biyu kuwa akwai wani.
9 But finally, there is the King who rules over the entire earth, which is subject to him.
Kowa yakan amfana da bunkasar amfanin ƙasa, sarki kansa yana samun riba daga gonaki.
10 A greedy man will not be satisfied by money. And whoever loves wealth will reap no fruit from it. Therefore, this, too, is emptiness.
Duk mai ƙaunar kuɗi ba ya samun isashe; duk ma ƙaunar dukiya ba ya ƙoshi da abin da yake samu. Wannan ma ba shi da amfani.
11 Where there are many riches, there will also be many to consume these things. And how does it benefit the one who possesses, except that he discerns the wealth with his own eyes?
Kamar yadda kaya suke haɓaka, haka ma masu amfani da su. Kuma wane amfani ne suke ga mai shi in ba ciyar da idanunsa a kansu ba?
12 Sleep is sweet to one who works, whether he consumes little or much. But the satiation of a wealthy man will not permit him to sleep.
Barcin ma’aikaci daɗi gare shi, ko yă ci kaɗan ko da yawa, amma yalwar mai arziki ba ta barinsa yă iya yin barci.
13 There is even another most burdensome infirmity, which I have seen under the sun: wealth kept to the harm of the owner.
Na ga wani mugun abu a duniya, arzikin da aka ajiye don yă cuce mai shi,
14 For they are lost in a most grievous affliction. He has produced a son, who will be in the utmost destitution.
ko kuwa dukiyar da ta ɓace ta wata hasara, har ya zama sa’ad da ya haifi ɗa, babu abin da ya bar masa.
15 Just as he went forth naked from his mother’s womb, so shall he return, and he shall take nothing with him from his labors.
Tsirara mutum yakan fito daga cikin mahaifiyarsa, kuma kamar yadda ya fito, haka zai koma. Ba ya ɗaukan kome daga wahalarsa da zai riƙe a hannunsa.
16 It is an utterly miserable infirmity that, in the same manner as he has arrived, so shall he return. How then does it benefit him, since he has labored for the wind?
Wannan ma mugun abu ne, Yadda mutum ya zo, haka zai koma, to, wace riba ce ya ci, da yake ya yi wahalar iska ce kawai?
17 All the days of his life he consumes: in darkness, and with many worries, and in distress as well as sadness.
Duk rayuwarsa ya ci abinci a cikin duhu, da ɓacin rai mai tsanani, da azaba, da fushi.
18 And so, this has seemed good to me: that a person should eat and drink, and should enjoy the fruits of his labor, in which he has toiled under the sun, for the number of the days of his life that God has given him. For this is his portion.
Sa’an nan na gane cewa abu mai kyau ne, daidai ne kuma mutum yă ci, yă sha, yă kuma ji daɗin aikin da ya yi a’yan kwanakin da Allah ya ba shi, gama wannan shi aka ƙaddara wa mutum daga faman wahalarsa a duniya a cikin’yan kwanakin da Allah ya ba shi a duniya, gama wannan shi ne rabonsa.
19 And this is a gift from God: that every man to whom God has given wealth and resources, and to whom he has granted the ability to consume these, may enjoy his portion, and may find joy in his labors.
Ban da haka ma, sa’ad da Allah ya ba wa mutum dukiya da wadata, ya kuma ba shi zarafi yă ji daɗinsu, ya kuma amince da rabonsa, sai yă ji daɗin aikinsa, wannan kyauta ce ta Allah.
20 And then he will not fully remember the days of his life, because God occupies his heart with delights.
Da ƙyar yake tunani a kan kwanakin rayuwarsa, domin Allah ya yarje masa, yă zauna da farin ciki.

< Ecclesiastes 5 >