< Ecclesiastes 3 >

1 All things have their time, and all things under heaven continue during their interval.
Akwai lokaci domin kowane abu, da kuma lokaci domin kowane aiki a duniya.
2 A time to be born, and a time to die. A time to plant, and a time to pull up what was planted.
Lokacin haihuwa da lokacin mutuwa, lokacin shuki da lokacin tumɓukewa.
3 A time to kill, and a time to heal. A time to tear down, and a time to build up.
Lokacin kisa da lokacin warkarwa, lokacin rushewa da lokacin ginawa.
4 A time to weep, and a time to laugh. A time to mourn, and a time to dance.
Lokacin kuka da lokacin dariya, lokacin makoki da lokacin rawa.
5 A time to scatter stones, and a time to gather. A time to embrace, and a time to be far from embraces.
Lokacin warwatsa duwatsu da lokacin tara su, lokacin runguma da lokacin dainawa.
6 A time to gain, and a time to lose. A time to keep, and a time to cast away.
Lokacin nema, da lokacin fid da zuciya, lokacin ajiyewa da lokacin zubarwa.
7 A time to rend, and a time to sew. A time to be silent, and a time to speak.
Lokacin yagewa da lokacin ɗinkewa, lokacin yin shiru da lokacin magana.
8 A time of love, and a time of hatred. A time of war, and a time of peace.
Lokacin ƙauna da lokacin ƙiyayya, lokacin yaƙi da lokacin salama.
9 What more does a man have from his labor?
Wace riba ce ma’aikaci yake da ita saboda wahalarsa?
10 I have seen the affliction that God has given to the sons of men, in order that they may be occupied by it.
Na ga nawayar da Allah ya ɗora a kan mutane.
11 He has made all things good in their time, and he has handed over the world to their disputes, so that man may not discover the work which God made from the beginning, even until the end.
Ya yi kowane abu da kyau a lokacinsa. Ya kuma sa matuƙa a zukatan mutane, duk da haka sun kāsa gane abin da Allah ya yi daga farko zuwa ƙarshe.
12 And I realize that there is nothing better than to rejoice, and to do well in this life.
Na san ba abin da ya fi wa mutane kyau fiye da su ji daɗi su kuma yi alheri yayinda suke da rai.
13 For this is a gift from God: when each man eats and drinks, and sees the good results of his labor.
Cewa kowa yă ci, yă sha, yă kuma ji daɗi cikin dukan aikinsa, wannan kyautar Allah ce.
14 I have learned that all the works which God has made continue on, in perpetuity. We are not able to add anything, nor to take anything away, from those things which God has made in order that he may be feared.
Na san cewa duk abin da Allah ya yi zai dawwama har abada; ba abin da za a ƙara ko a rage. Allah ya yi haka domin mutane su girmama shi.
15 What has been made, the same continues. What is in the future, has already existed. And God restores what has passed away.
Duk abin da yana nan ya taɓa kasancewa, kuma abin da zai kasance, ya taɓa kasancewa; Allah kuma zai nemi bayanin abubuwan da suka wuce.
16 I saw under the sun: instead of judgment, impiety, and instead of justice, iniquity.
Sai na ga wani abu kuma a duniya, a wurin shari’a, akwai mugunta a can, a wurin adalci, akwai mugunta a can.
17 And I said in my heart: “God will judge the just and the impious, and then the time for each matter shall be.”
Sai na yi tunani a zuciyata, “Allah zai shari’anta masu adalci da masu mugunta, gama za a kasance da lokaci domin kowane aiki, lokaci domin kowane abu.”
18 I said in my heart, about the sons of men, that God would test them, and reveal them to be like wild animals.
Na sāke yin tunani, “Game da mutane kam, Allah kan gwada su don su san cewa ba su fi dabba ba.
19 For this reason, the passing away of man and of beasts is one, and the condition of both is equal. For as a man dies, so also do they die. All things breathe similarly, and man has nothing more than beast; for all these are subject to vanity.
Ƙaddarar mutum ɗaya take da ta dabba; ƙaddara ɗaya ce take jiransu biyu. Yadda ɗayan yake mutuwa, haka ma ɗayan. Dukansu numfashinsu iri ɗaya ne; mutum bai fi dabba ba. Kowane abu ba shi da amfani.
20 And all things continue on to one place; for from the earth they were made, and unto the earth they shall return together.
Duka wuri ɗaya za su tafi; gama duka daga turɓaya suka fito, kuma ga turɓaya duka za su koma.
21 Who knows if the spirit of the sons of Adam ascend upward, and if the spirit of the beasts descend downward?
Wa ya tabbatar cewa ruhun mutum yakan tashi sama sa’an nan na dabba yă sauka ƙasa?”
22 And I have discovered nothing to be better than for a man to rejoice in his work: for this is his portion. And who shall add to him, so that he may know the things that will occur after him?
Saboda haka na ga babu abin da ya fi kyau wa mutum fiye da yă more wahalar aikinsa, domin wannan ne rabonsa. Gama wa zai kawo shi yă ga abin da zai faru a bayansa?

< Ecclesiastes 3 >