< Deuteronomy 3 >

1 “And so, having turned back, we ascended by the way of Bashan. And Og, the king of Bashan, went forth with his people to meet us in warfare at Edrei.
Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
2 And the Lord said to me: ‘You should not fear him. For he has been delivered into your hand, with all his people as well as his land. And you shall do to him just as you have done to Sihon, the king of the Amorites, who lived at Heshbon.’
Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
3 Therefore, the Lord our God delivered into our hands, now Og, the king of Bashan, and all his people. And we struck them down unto utter annihilation,
Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
4 laying waste to all his cities at one time. There was not a village which escaped from us: sixty cities, the entire region of Argob, the kingdom of Og, in Bashan.
A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
5 All the cities were fortified with very high walls, and with gates and bars, in addition to innumerable villages which had no walls.
Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
6 And we wiped them out, just as we had done to Sihon, the king of Heshbon, destroying every city, and its men, as well as women and children.
Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
7 But the cattle and the spoils of the cities, we plundered.
Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
8 And at that time, we took the land from the hand of the two kings of the Amorites, who were across the Jordan: from the torrent Arnon as far as Mount Hermon,
A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
9 which the Sidonians call Sirion, and the Amorites call Senir,
(Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
10 all the cities that are situated in the plain, and the entire land of Gilead and Bashan, all the way to Salecah and Edrei, cities of the kingdom of Og in Bashan.
Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
11 For only Og, the king of Bashan, was left behind out of the race of the giants. His bed of iron is on display, (it is in Rabbah, among the sons of Ammon) being nine cubits in length, and four in width, according to the measure of the cubit of a man’s hand.
(Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
12 And we possessed the land, at that time, from Aroer, which is above the bank of the torrent Arnon, as far as the middle of Mount Gilead. And I gave its cities to Ruben and Gad.
Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
13 Then I delivered the remaining part of Gilead, and all of Bashan, the kingdom of Og, which is the entire region of Argob, to one half of the tribe of Manasseh. And all of Bashan is called the land of the giants.
Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
14 Jair, the son of Manasseh, possessed all the region of Argob, as far as the borders of Geshur and Maacath. And he called Bashan by his own name, Havvoth Jair, that is, the villages of Jair, even to the present day.
Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
15 Likewise, to Machir, I gave Gilead.
Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
16 And to the tribes of Ruben and Gad, I gave from the land of Gilead as far as the torrent Arnon, one half of the torrent and its confines, even to the torrent Jabbok, which is along the border of the sons of Ammon,
Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
17 and the plain of the wilderness, as well as the Jordan, and the borders of Chinnereth, all the way to the sea of the desert, which is very salty, to the base of Mount Pisgah toward the east.
Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
18 And I instructed you at that time, saying: ‘The Lord your God gives to you this land as an inheritance. Having armed yourselves, go before your brothers, the sons of Israel, all you strong men.
Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
19 Leave behind your wives and little ones, as well as the cattle. For I know that you have many cattle, and they should remain in the cities which I have delivered to you,
Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
20 until the Lord provides rest to your brothers, just as he has provided for you. And they, too, shall possess the land, which he will give to them beyond the Jordan. Then each one shall return to his possession, which I have allotted to you.’
sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
21 Likewise, I instructed Joshua at that time, saying: ‘Your eyes have seen what the Lord your God has done to these two kings. So also will he do to all the kingdoms through which you shall pass.
A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
22 You should not fear them. For the Lord your God will fight on your behalf.’
Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
23 And I beseeched the Lord at that time, saying:
A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
24 ‘Lord God, you have begun to reveal your greatness and your very strong hand to your servant. For there is no other god, either in heaven or on earth, who is able to accomplish your works, or to be compared to your strength.
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
25 Therefore, I will cross over, and I will view this excellent land beyond the Jordan, and this singular mountain, and Lebanon.’
Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
26 And the Lord became angry with me because of you, and he would not heed me. But he said to me: ‘It is enough for you. You shall no longer speak to me at all about this matter.
Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
27 Ascend to the summit of Pisgah, and look around with your eyes to the west, and to the north, and to the south, and to the east, and behold it. For you shall not cross this Jordan.
Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
28 Instruct Joshua, and encourage and strengthen him. For he shall go before this people, and he shall distribute to them the land that you will see.’
Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
29 And we remained in the valley, opposite the shrine of Peor.”
Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.

< Deuteronomy 3 >