< Deuteronomy 27 >

1 Then Moses and the elders of Israel instructed the people, saying: “Keep each commandment that I instruct to you this day.
Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
2 And when you have crossed over the Jordan, into the land which the Lord your God will give to you, you shall erect immense stones, and you shall coat them with plaster,
Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
3 so that you may be able to write upon them all the words of this law, when you have crossed the Jordan so as to enter into the land which the Lord your God will give to you, a land flowing with milk and honey, just as he swore to your fathers.
Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
4 Therefore, when you have crossed over the Jordan, erect the stones, just as I instruct you to do this day, on Mount Ebal. And you shall coat them with plaster,
Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
5 and you shall build, in that place, an altar to the Lord your God out of stones which have not been touched by iron,
Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
6 out of stones which have not been hewn or polished. And you shall offer holocausts on it to the Lord your God.
Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
7 And you shall immolate peace victims. And you shall eat and feast in that place, in the sight of the Lord your God.
Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
8 And you shall write upon the stones all the words of this law, plainly and clearly.”
Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
9 And Moses and the priests of Levitical stock said to all of Israel: “Attend and listen, O Israel! Today you have become the people of the Lord your God.
Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
10 You shall listen to his voice, and you shall do the commandments and justices, which I am entrusting to you.”
Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
11 And Moses instructed the people in that day, saying:
A wannan rana Musa ya umarce mutane,
12 “These shall stand upon Mount Gerizim, as a blessing to the people, when you will have crossed the Jordan: Simeon, Levi, Judah, Issachar, Joseph, and Benjamin.
Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
13 And in the opposite region, there shall stand upon Mount Ebal, as a curse: Reuben, Gad, and Asher, and Zebulun, Dan, and Naphtali.
Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
14 And the Levites shall pronounce and declare to all the men of Israel, with an exalted voice:
Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
15 Cursed be the man who makes a graven or molten idol, an abomination to the Lord, a work of the hands of its maker, and who puts it in a secret place. And all the people shall respond by saying: Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
16 Cursed be he who does not honor his father and mother. And all the people shall say: Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
17 Cursed be he who removes his neighbor’s landmarks. And all the people shall say: Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
18 Cursed be he who causes the blind to go astray on a journey. And all the people shall say: Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
19 Cursed be he who subverts the judgment of the new arrival, the orphan, or the widow. And all the people shall say: Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
20 Cursed be he who lies with his father’s wife, and so exposes the covering of his bed. And all the people shall say: Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
21 Cursed be he who lies with any beast. And all the people shall say: Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
22 Cursed be he who lies with his sister, the daughter of his father, or of his mother. And all the people shall say: Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
23 Cursed be he who lies with his mother-in-law. And all the people shall say: Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
24 Cursed be he who secretly strikes down his neighbor. And all the people shall say: Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
25 Cursed be he who accepts gifts in order to strike down the life of innocent blood. And all the people shall say: Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
26 Cursed be he who does not remain in the words of this law, and does not carry them out in deed. And all the people shall say: Amen.”
“La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”

< Deuteronomy 27 >