< Deuteronomy 24 >

1 “If a man takes a wife, and he has her, and she does not find favor before his eyes because of some vileness, then he shall write a bill of divorce, and he shall give it to her hand, and he shall dismiss her from his house.
Idan mutum ya auri mata, daga baya ba tă gamshe shi ba domin ya gano wani abu marar kyau game da ita, ya ba ta takardar saki, ya kuma kore ta daga gidansa,
2 And when, having departed, she has married another,
in bayan ta bar gidansa ta zama matar wani dabam,
3 and if he likewise hates her, and has given her a bill of divorce, and has dismissed her from his house, or if indeed he has died,
sai mijinta na biyu ya ƙi ta, ya ba ta takardan saki, ya kore ta daga gidansa, ko kuwa ya mutu,
4 then the former husband cannot take her back as a wife. For she has been polluted and has become abominable in the sight of the Lord. Otherwise, you may cause your land, which the Lord your God will deliver to you as a possession, to sin.
to, kada mijinta na farko, wanda ya sake ta yă sāke aurenta, tun da yake ta ƙazantu. Wannan zai zama abin ƙyama a gaban Ubangiji. Kada ku kawo zunubi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo.
5 When a man has recently taken a wife, he shall not go out to war, nor shall any public office be enjoined upon him. Instead, he shall be free at home without guilt, so that for one year he may rejoice with his wife.
In mutum bai daɗe da aure ba, kada a sa yă je yaƙi, ko yă yi wani aiki. Gama zai huta shekara guda a gida, yă faranta wa matar da ya aura rai.
6 You shall not accept an upper or lower millstone as collateral. For then he will have placed his life with you.
Kada ku karɓi jinginar dutsen niƙa tare da ɗan dutsen niƙan, domin yin haka zai zama karɓar jinginar rai ne.
7 If a man has been caught soliciting his brother among the sons of Israel, and selling him in order to receive a price, then he shall be put to death. And so shall you take away the evil from your midst.
Idan aka kama wani yana satar ɗan’uwansa mutumin Isra’ila domin yă sa ya zama bawansa, ko yă sayar da shi, sai a kashe ɓarawon nan. Haka za ku kawar da mugunta daga cikinku.
8 Observe diligently, lest you incur the wound of leprosy. But you shall do whatever the priests of the Levitical stock shall teach you to do, according to what I have instructed them. And you shall fulfill it carefully.
Game da cututtukan kuturta, sai ku lura, ku yi yadda firistocin da suke Lawiyawa suka umarce ku. Dole ku lura ku bi abin da na umarce su.
9 Remember what the Lord your God did to Miriam, along the way, as you were departing from Egypt.
Ku tuna da abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Miriyam a hanya, bayan kun fito Masar.
10 When you require from your neighbor anything that he owes to you, you shall not enter into his house in order to take away the collateral.
Sa’ad da kuka ba da rance na kowane iri ga maƙwabcinku, kada ku shiga gidansa don karɓar wani abu a matsayin jingina.
11 Instead, you shall stand outside, and he will carry out to you what he has.
Ku tsaya a waje ku bar mutumin da yake karɓan rancen yă kawo muku abin da zai bayar a matsayin jingina.
12 But if he is poor, then the collateral shall not remain with you through the night.
In matalauci ne, kada ku kwana da abin da zai bayar a matsayin jingina a wurinku.
13 Instead, you shall return it to him promptly, before the setting of the sun, so that, sleeping in his own garment, he may bless you, and you may have justice in the presence of the Lord your God.
Ku mayar da rigarsa a fāɗuwar rana saboda yă sami abin rufuwa. Yin haka zai sa yă gode muku, za a kuma ɗauka wannan a matsayin aikin adalci da kuka yi a gaban Ubangiji Allahnku.
14 You shall not refuse the pay of the indigent and the poor, whether he is your brother, or he is a new arrival who dwells with you in the land and is within your gates.
Kada ku zalunci ɗan ƙodago matalauci da mabukaci, ko da shi ɗan’uwanku ne mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a cikin garuruwanku.
15 Instead, you shall pay him the price of his labor on the same day, before the setting of the sun. For he is poor, and with it he sustains his life. Otherwise, he may cry out against you to the Lord, and it would be charged to you as a sin.
Ku biya kuɗin aikinsa kowace rana kafin fāɗuwar rana, domin shi matalauci ne, yana kuma sa rai a kan wannan hakkin ne, don kada ya yi wa Ubangiji kuka a kanku, har yă zama laifi a gare ku.
16 The fathers shall not be put to death on behalf of the sons, nor the sons on behalf of the fathers, but each one shall die for his own sin.
Ba za a kashe iyaye a maimakon’ya’yansu ba, ba kuwa za a kashe’ya’ya a maimakon iyayensu ba; kowa ya yi zunubi, shi za a kashe.
17 You shall not pervert the judgment of the new arrival or the orphan, nor shall you take away the widow’s garment as collateral.
Ba za ku danne hakkin baƙon da yake zama a cikinku ko na marayu ba, ba za ku ɗauki rigar matar da mijinta ya mutu a matsayin jingina ba.
18 Remember that you served in Egypt, and that the Lord your God rescued you from there. Therefore, I am instructing you to act in this way.
Ku tuna dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuwa ya fisshe daga can. Shi ya sa na umarce ku ku yi wannan.
19 When you have reaped the grain in your field, and, having forgotten, you leave behind a sheaf, you shall not return to take it away. Instead, you shall permit the new arrival, and the orphan, and the widow to take it away, so that the Lord your God may bless you in all the works of your hands.
Sa’ad da kuke girbi a gonarku, sai kuka manta da dami, kada ku koma don ku ɗauka. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa, saboda Ubangiji Allahnku yă albarkace ku a cikin dukan aikin hannuwanku.
20 If you have gathered the fruit of your olive trees, you shall not return in order to gather whatever may remain on the trees. Instead, you shall leave it behind for the new arrival, the orphan, and the widow.
Sa’ad da kuka kakkaɓe’ya’yan zaitun daga itatuwanku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
21 If you harvest the vintage of your vineyard, you shall not gather the remaining clusters. Instead, they shall fall to the use of the stranger, the orphan, and the widow.
Sa’ad da kuka yi girbin inabi a gonar inabinku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
22 Remember that you also served in Egypt, and so, for this reason, I am instructing you to act in this way.”
Ku tuna dā ku bayi ne Masar. Shi ya sa na umarce ku ku yi wannan.

< Deuteronomy 24 >