< Deuteronomy 2 >

1 “And setting out from there, we arrived at the wilderness which leads to the Red Sea, just as the Lord had spoken to me. And we encompassed Mount Seir for a long time.
Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
2 And the Lord said to me:
Sai Ubangiji ya ce mini,
3 ‘You have encompassed this mountain for long enough. Go forth, toward the north.
“Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
4 And instruct the people, saying: You shall cross through the borders of your brothers, the sons of Esau, who live at Seir, and they will fear you.
Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
5 Therefore, take care diligently, lest you be moved against them. For I will not give to you from their land even as much as the step that one foot can tread upon, because I have given Mount Seir to Esau as a possession.
kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
6 You shall buy food from them for money, and you shall eat. You shall draw water for money, and you shall drink.
Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
7 The Lord your God has blessed you in every work of your hands. The Lord your God, dwelling with you, knows your journey, how you crossed through this great wilderness over forty years, and how you have been lacking in nothing.’
Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
8 And when we had passed through our brothers, the sons of Esau, who were living at Seir by the way of the plain from Elath and from Eziongeber, we arrived at the way which leads to the desert of Moab.
Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
9 And the Lord said to me: ‘You should not fight against the Moabites, nor should you go to battle against them. For I will not give to you anything from their land, because I have given Ar to the sons of Lot as a possession.’
Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
10 The Emim were the first of its inhabitants, a people great and strong, and of such great height, like the race of the Anakim.
(Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
11 They were considered to be like giants, and they were like the sons of the Anakim. And, indeed, the Moabites call them: the Emim.
Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
12 The Horites also formerly lived at Seir. When these had been driven out and destroyed, the sons of Esau lived there, just as Israel did in the land of his possession, which the Lord gave to him.
Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
13 Then, rising up so as to cross over the torrent Zered, we arrived at the place.
Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
14 Then, from the time that we advanced from Kadesh-barnea until we crossed over the torrent Zered, there were thirty-eight years, until the entire generation of the men who were fit for war had been consumed out of the camp, just as the Lord had sworn.
Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
15 For his hand was against them, so that they would pass away from the midst of the camp.
Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
16 Then, after all the fighting men had fallen,
To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
17 the Lord spoke to me, saying:
sai Ubangiji ya ce mini,
18 ‘Today, you shall cross the borders of Moab, at the city named Ar.
“Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
19 And when you have arrived in the vicinity of the sons of Ammon, be careful that you do not fight against them, nor should you be moved to battle. For I will not give to you from the land of the sons of Ammon, because I have given it to the sons of Lot as a possession.’
Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
20 It was reputed to be a land of giants. And giants lived there in times past, those whom the Ammonites call the Zamzummim.
(Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
21 They are a people, great and numerous, and of lofty stature, like the Anakim, whom the Lord wiped away before their face. And he caused them to live there in place of them,
Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
22 just as he had done for the sons of Esau, who live at Seir, wiping out the Horites and delivering their land to them, which they possess even to the present time.
Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
23 Likewise the Hevites, who were living in small villages as far as Gaza, were expelled by the Cappadocians, who went forth from Cappadocia, and they wiped them out and lived in their place.
Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
24 ‘Rise up and cross the torrent Arnon! Behold, I have delivered Sihon, the king of Heshbon, the Amorite, into your hand, and so, begin to possess his land and to engage in battle against him.
“Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
25 Today I will begin to send the terror and dread of you among the peoples who are living under all of heaven, so that, when they hear your name, they may be afraid, and may tremble in the manner of a woman giving birth, and may be gripped by anguish.’
A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
26 Therefore, I sent messengers from the wilderness of Kedemoth to Sihon, the king of Heshbon, with peaceful words, saying:
Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
27 ‘We will cross through your land. We will advance by the public way. We will not turn aside, neither to the right, nor to the left.
“Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
28 Sell us food for a price, so that we may eat. Provide us with water for money, and so we will drink. We only ask that you allow us to pass through,
Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
29 just as the sons of Esau have done, who live at Seir, and the Moabites, who abide in Ar, until we arrive at the Jordan, and we cross to the land which the Lord our God will give to us.’
kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
30 And Sihon, the king of Heshbon, was not willing to grant passage to us. For the Lord your God had hardened his spirit, and had fastened his heart, so that he would be delivered into your hands, just as you now see.
Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
31 And the Lord said to me: ‘Behold, I have begun to deliver Sihon and his land to you. Begin to possess it.’
Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
32 And Sihon went out to meet us with all his people, to battle at Jahaz.
Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
33 And the Lord our God delivered him to us. And we struck him down, with his sons and all his people.
sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
34 And we seized all his cities at that time, putting to death their inhabitants: men as well as women and children. We left nothing of them,
A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
35 except the cattle, which went to the share of those who plundered them. And we seized the spoils of the cities,
Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
36 from Aroer, which is above the bank of the torrent Arnon, a town which is situated in a valley, all the way to Gilead. There was not a village or city which escaped from our hands. The Lord our God delivered everything to us,
Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
37 except the land of the sons of Ammon, which we did not approach, and all that is adjacent to the torrent Jabbok, and the cities in the mountains, and all the places which the Lord our God prohibited to us.”
Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.

< Deuteronomy 2 >