< Daniel 8 >

1 In the third year of the reign of Belshazzar the king, a vision appeared to me. After that which I had seen in the beginning, I, Daniel,
A shekara ta uku ta mulkin sarki Belshazar, ni, Daniyel, na ga wahayi, bayan wancan da na riga gani.
2 saw in my vision, that I was in the capital city of Susa, which is in the region of Elam, yet I saw in the vision that I was over the gate of Ulai.
A cikin wahayin, na ga kaina a mafakar Shusha a yankin Elam; a wahayin na ga ina a bakin Kogin Ulai.
3 And I lifted up my eyes and saw, and behold, a single ram stood before the marsh, having two high horns, and one was higher than the other and growing higher still.
Na ɗaga ido, a gabana kuwa sai ga rago mai ƙahoni biyu, yana tsaye a gefen mashigin kogin, ƙahonin kuma suna da tsawo. Ɗaya daga cikin ƙahonin ya fi ɗayan tsawo. Wanda ya fi tsawon shi ne ya tsiro daga baya.
4 After this, I saw the ram brandishing his horns against the West, and against the North, and against the Meridian, and all the beasts could not withstand him, nor be freed from his hand, and he did according to his own will, and he became great.
Na lura da ragon sa’ad da ya kai karo wajen yamma da arewa da kudu. Babu wata dabbar da ta iya ƙarawa da shi, babu kuma wanda ya iya kuɓuta daga ikonsa. Ya yi yadda ya ga dama, ya kuma zama mai girma.
5 And I understood, and behold, a he-goat among she-goats came from the West above the face of the entire earth, and he did not touch the ground. Furthermore, the he-goat had a preeminent horn between his eyes.
Yayinda nake tunani game da wannan, farat ɗaya sai ga bunsurun da yake da sanannen ƙaho tsakanin idanunsa ya ɓullo daga wajen yamma, yana ratsa dukan duniya ba ya ko taɓa ƙasa.
6 And he went all the way to the ram that had the horns, which I had seen standing before the gate, and he ran towards him in the force of his strength.
Ya zo wajen rago mai ƙahoni biyu ɗin nan da na riga na gani tsaye a gefen mashigin kogin nan ya tasar masa da fushi mai zafi.
7 And when he approached near to the ram, he was enraged against him, and he struck the ram, and broke his two horns, and the ram could not withstand him, and when he had cast him down on the ground, he trampled him, and no one was able to free the ram from his hand.
Na ga ya zo kusa da ragon, ya husata da shi ƙwarai, ya kai wa ragon hari. Ya kakkarya ƙahoninsa nan biyu. Ƙarfin ragon ya kāsa, bai iya kāre kansa daga bunsurun ba. Bunsurun ya buge shi ƙasa ya tattake shi. Ba wanda ya iya ceton ragon daga bunsurun.
8 But the he-goat among she-goats became exceedingly great, and when he had prospered, the great horn was shattered, and four horns were rising up beneath it by means of the four winds of heaven.
Bunsurun kuwa ya ƙasaita, amma a ƙwanƙolin ikonsa sai aka karye babban ƙahonsa, kuma a wurin da ƙahon nan ya kasance waɗansu sanannun ƙahoni huɗu suka tsiro suna fuskantar kusurwoyin nan huɗu.
9 But from one of them came forth one little horn, and it became great against the Meridian, and against the East, and against the strength.
Daga cikin ɗayansu kuma wani ƙaramin ƙaho ya fito, ya yi girma ya ƙasaita ƙwarai zuwa kudu da kuma gabas da wajen Kyakkyawar Ƙasa.
10 And it was magnified even towards the strength of heaven, and it threw down those of the strength and of the stars, and it trampled them.
Ya yi girma sai da ya kai rundunar sammai, ya kuma fid da waɗansu rundunar taurari zuwa ƙasa ya kuma tattake su.
11 And it was magnified, even to the leader of the strength, and it took away from him the continual sacrifice, and cast down the place of his sanctuary.
Sai ya ɗora kansa ya zama mai girma kamar Sarkin runduna; sai aka ɗauke hadaya ta kullayaumi daga gare shi, aka kuma saukar da wurin masujadarsa ƙasa.
12 And the advantage was given to him against the continual sacrifice, because of the sins, and truth will be struck down to the ground, and he will act, and he will prosper.
Saboda tawaye, sai aka ba da rundunar tsarkaka da kuma hadayar ƙonawa ta kowace rana ga ƙahon. Sai ya yi watsi da gaskiya, ya yi abin da ya ga dama, ya kuwa yi nasara.
13 And I heard one of the holy ones speaking, and one saint said to another, (I know not to whom he was speaking, ) “What is the extent of the vision, and the continual sacrifice, and the sin of the desolation, which has happened, and of the sanctuary and the strength, which will be trampled?”
Sa’an nan na ji mai tsarkin nan yana magana, wani mai tsarki kuma ya ce da wancan, “Har yaushe wannan wahayi zai tabbata, wahayi game da hadaya ta kullayaumi, da tawayen da yake kawo lalacewa, da kuma miƙa wuri mai tsarki da kuma na rundunar da za a tattake a ƙarƙashin sawu?”
14 And he said to him, “From evening until morning, two thousand three hundred days, and so the sanctuary will be cleansed.”
Sai ya ce mini, “Zai ɗauki safiya da yamma 2,300; sa’an nan za a sāke tsarkake wuri mai tsarki.”
15 But it came to pass, when I, Daniel, saw the vision and sought understanding that, behold, there stood in my sight something like the appearance of a man.
Yayinda ni, Daniyel, nake duban wahayi ina ƙoƙari in fahimce shi, sai ga wani a gabana wanda ya yi kama da mutum.
16 And I heard the voice of a man within Ulai, and he called out and said, “Gabriel, make this one understand the vision.”
Sai na ji muryar wani mutum daga Ulai tana cewa, “Jibra’ilu, faɗa wa wannan mutum ma’anar wahayin.”
17 And he came and stood next to where I was standing, and when he approached, I fell on my face, trembling, and he said to me, “Understand, son of man, for in the time of the end the vision will be fulfilled.”
Da ya zo kusa da inda nake tsaye, na firgita na kuma fāɗi rubda ciki. Ya ce da ni “Ɗan mutum, ka gane da cewa wannan wahayi yana magana ne a kan kwanakin ƙarshe.”
18 And when he spoke to me, I fell forward onto the ground, and so he touched me and stood me upright.
Yayinda yake magana da ni, barci mai nauyi ya kwashe ni, da nake kwance rubda ciki. Sai ya taɓa ni ya kuma tashe ni tsaye.
19 And he said to me, “I will reveal to you what the future things are in the earlier tribulation, for the time has its end.
Sai ya ce, “Zan faɗa maka abin da zai faru a lokacin fushi, saboda wahayin yana magana ne a kan lokacin da aka ƙayyade na ƙarshe.
20 The ram, which you saw to have horns, is the king of the Medes and Persians.
Rago mai ƙahoni biyu da ka gani, yana a madadin sarakunan Medes da Farisa ne.
21 Furthermore, the he-goat among she-goats is the king of the Greeks, and the great horn, which was between his eyes, is the same one, the first king.
Bunsurun kuwa sarkin Girka ne, kuma babban ƙahon da yake tsakanin idanunsa, sarki na farko ne.
22 And since, having been shattered, there grew four in its place, four kings will rise up from his people, but not in his strength.
Ƙahoni huɗu da suka maya wannan da ya karye yana a madadin masarautu huɗu da za su tashi daga cikin al’ummarsa amma ba za su sami irin ikonsa ba.
23 And after their reign, when iniquities will be increased, there will arise a king of shameless face and understanding negotiations.
“Can wajen ƙarshe mulkinsu, sa’ad da muguntarsu ta kai intaha, wani mugun sarki mai rashin hankali, uban makirci, zai fito.
24 And his advantage will be strengthened, but not by his kind of force, and other than what he will be able to trust, everything will be eradicated, and he will prosper, and he will act. And he will execute the successful and the people of the saints,
Zai yi ƙarfi ƙwarai da gaske, amma ba da ikonsa ba. Zai jawo mummunar hallakarwa kuma zai yi nasara a duk abin da ya sa gaba. Zai hallakar da majiya ƙarfi da kuma tsarkaka.
25 according to his will, and treachery will be guided by his hand. And his heart will be inflated, and by the abundance of everything he will kill many, and he will rise up against the Lord of lords, and he will be knocked down without a hand.
Zai sa yaudara ta ƙara yin yawa, zai ɗaukaka kansa. Sa’ad da suke ji sun sami mafaka, zai hallaka mutane da yawa sa’an nan kuma yă fara gāba da Sarkin sarakuna. Duk da haka za a hallaka shi, amma ba da ikon mutum ba.
26 And the vision of the evening and the morning, which was told, is true. Therefore, you must seal the vision, because, after many days, it will occur.”
“Wahayin nan na safiya da yamma da aka nuna maka gaskiya ne, amma ka ɓoye wahayin, gama ya shafi nan gaba mai tsawo ne.”
27 And I, Daniel, languished and was sick for some days, and when I had lifted myself up, I performed the king’s works, and I was astonished at the vision, and there was none who could interpret it.
Ni, Daniyel, na gaji matuƙa na kuma yi rashin lafiya na kwanaki masu yawa. Sa’an nan sai na tashi na ci gaba da hidimar sarki. Wahayin ya shige mini duhu, ya fi ƙarfin fahimtata.

< Daniel 8 >