< Amos 8 >

1 These things the Lord has revealed to me. And behold, a hook to draw down fruit.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji ya nuna mini kwandon nunannun’ya’yan itace.
2 And he said, “What do you see, Amos?” And I said, “A hook to draw down fruit.” And the Lord said to me, “The end has come for my people Israel. I will no longer pass through them.”
Ya yi tambaya ya ce, “Me ka gani Amos?” Sai na amsa na ce, “Kwandon nunannun’ya’yan itace.” Sai Ubangiji ya ce mini, “Lokaci ya yi wa mutanena Isra’ila da ba zan ƙara barinsu ba.
3 And the hinges of the temple will creak in that day, says the Lord God. Many will die. Silence will be thrown away in all places.
“A ranan nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Waƙoƙin a haikali za su koma makoki. Za a ga gawawwaki a ko’ina! Shiru!”
4 Hear this, you who crush the poor and who make those in need of land to do without.
Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata kuka kori matalautan ƙasar.
5 You say, “When will the first day of the month be over, so we can sell our wares, and the Sabbath, so we can open the grain: in order that we may decrease the measure, and increase the price, and substitute deceitful scales,
Kuna cewa, “Yaushe Sabon Wata zai wuce don mu sayar da hatsi, Asabbaci ta wuce, don mu sayar da alkama?” Mu yi awo da ma’aunin zalunci mu ƙara kuɗin kaya mu kuma cutar da mai saya,
6 in order that we may possess the destitute with money, and the poor for a pair of shoes, and may sell even the refuse of the grain?”
mu sayi matalauta da azurfa masu bukata kuma da takalmi, mu sayar da alkamar haɗe da yayi.
7 The Lord has sworn by the arrogance of Jacob: I will not forget, even to the end, all their works.
Ubangiji ya rantse da Girman Yaƙub, “Ba zan taɓa mantawa da duk wani abin da suka yi ba.
8 Will not the earth shudder over this, and all its inhabitants mourn, and all rise up like a river, and be cast out, and flow away like the river of Egypt?
“Shin, ƙasar ba za tă yi rawan jiki saboda wannan ba, kuma duk masu zama a cikinta ba za su yi makoki ba? Ƙasar duka za tă hau ta sauka kamar Nilu; za a dama ta sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar.
9 And it will be in that day, says the Lord God, that the sun will decline at midday, and I will cause the earth to become dark on the day of light.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Zan sa rana ta fāɗi da tsakar rana in kuma duhunta duniya da rana tsaka.
10 And I will turn your feasts into mourning, and all your hymns into lamentation. And I will put sackcloth over every one of your backs, and baldness on every head. And I will begin it like the mourning for an only-begotten son, and complete it like a bitter day.
Zan mai da bukukkuwanku na addini su zama makoki kuma dukan waƙoƙinku su zama kuka. Zan sa dukanku ku sa rigunan makoki za ku kuma aske kawunanku. Zan sa wannan lokaci yă zama kamar lokacin da ake makokin ɗan tilon da ake da shi kuma ƙarshenta kamar rana mai ɗaci.
11 Behold, the days pass, says the Lord, and I will send a famine on the earth: not a famine of bread, nor of thirst for water, but for hearing the word of the Lord.
“Ranakun suna zuwa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “sa’ad da zan aika da yunwa cikin ƙasar, ba yunwar abinci ko ta ƙishirwa ba, sai dai yunwa ta jin maganar Ubangiji.
12 And they will move even from sea to sea, and from the North all the way to the East. They will wander around seeking the word of the Lord, and they will not find it.
Mutane za su yi ta tangaɗi daga teku zuwa teku suna yawo daga arewa zuwa kudu, suna neman maganar Ubangiji, amma ba za su samu ba.
13 In that day, beautiful virgins, and young men, will fail because of thirst.
“A wannan rana “kyawawan’yan mata da kuma samari masu ji da ƙarfi za su suma don ƙishirwa.
14 They swear by the offense of Samaria, and they say, “As your God lives, Dan,” and “The way of Beer-sheba lives.” And they will fall, and they will not rise up any more.
Waɗanda suka yi rantsuwa da abin kunya na Samariya, ko kuma su ce, ‘Muddin allahnku yana a raye, ya Dan,’ ko kuwa, ‘Muddin allahn Beyersheba yana a raye,’ za su fāɗi, ba kuwa za su ƙara tashi ba.”

< Amos 8 >