< 2 Samuel 9 >

1 And David said, “Do you think that there could be anyone left from the house of Saul, so that I might show mercy to him because of Jonathan?”
Wata rana Dawuda ya yi tambaya ya ce, “Akwai wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu wanda zan nuna masa alheri saboda Yonatan?”
2 Now there was, from the house of Saul, a servant named Ziba. And when the king had called him to himself, he said to him, “Are you not Ziba?” And he responded, “I am your servant.”
To, akwai wani bawa na gidan Shawulu mai suna Ziba. Sai aka kira shi yă bayyana a gaban Dawuda, sarki ya ce masa, “Kai ne Ziba?” Sai ya ce, “I, ni ne, ranka yă daɗe.”
3 And the king said, “Could there be anyone alive from the house of Saul, so that I may show the mercy of God to him?” And Ziba said to the king, “There is left alive a son of Jonathan, with disabled feet.”
Sa’an nan sarki ya yi tambaya ya ce, “Babu wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu don in nuna masa alherin Allah?” Ziba ya ce wa sarki, “Har yanzu akwai ɗan Yonatan da ya rage, sai dai shi gurgu ne a dukan ƙafafu.”
4 “Where is he?” he said. And Ziba said to the king, “Behold, he is in the house of Machir, the son of Ammiel, in Lodebar.”
Sarki ya ce, “Ina yake?” Ziba ya ce, “Yana a gidan Makir ɗan Ammiyel a Lo Debar.”
5 Therefore, king David sent and brought him from the house of Machir, the son of Ammiel, from Lodebar.
Saboda haka Sarki Dawuda ya umarta aka kawo shi daga gidan Makir ɗan Ammiyel, daga Lo Debar.
6 And when Mephibosheth, the son of Jonathan, the son of Saul, had come to David, he fell upon his face, and he reverenced. And David said, “Mephibosheth?” And he responded, “Your servant is here.”
Sa’ad da Mefiboshet ɗan Yonatan, ɗan Shawulu, ya zo wurin Dawuda, sai ya rusuna har ƙasa ya yi gaisuwar bangirma. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!” Shi kuwa ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, ga ni, bawanka.”
7 And David said to him: “Do not be afraid. For I will certainly show mercy to you because of your father Jonathan. And I will restore to you all the fields of your father Saul. And you shall eat bread at my table always.”
Dawuda ya ce, “Kada ka ji tsoro, gama tabbatacce zan nuna maka alheri saboda mahaifinka Yonatan. Zan mayar maka da dukan ƙasar da take ta kakanka Shawulu, kullum kuma za ka ci a teburina.”
8 And reverencing him, he said, “Who am I, your servant, that you should look with favor upon a dead dog like me?”
Mefiboshet ya rusuna ya ce, “Ni ne wa har da za ka kula da ni? Ai! Ni bawanka ne da bai ma fi mataccen kare daraja ba.”
9 And so, the king called Ziba, the servant of Saul, and he said to him: “Everything whatsoever that belonged to Saul, and his entire house, I have given to the son of your lord.
Sai sarki ya kira Ziba bawan Shawulu, ya ce masa, “Na ba wa jikan maigidanka kome da yake na Shawulu da iyalinsa
10 And so, work the land for him, you and your sons and your servants. And you shall bring in food for the son of your lord, for nourishment. And Mephibosheth, the son of your lord, shall always eat bread at my table.” Now Ziba had fifteen sons and twenty servants.
Kai da’ya’yanka maza da bayinka za ku riƙa yin masa noma, ku kuma kawo hatsin, don jikan maigidanka yă sami abinci. Mefiboshet kuma, jikan maigidanka, zai riƙa ci a teburina.” (Ziba kuwa yana da’ya’ya maza goma sha biyar da kuma bayi ashirin.)
11 And Ziba said to the king: “Just as my lord has ordered your servant, so will your servant do. And Mephibosheth shall eat at my table, like one of the sons of the king.”
Sai Ziba ya ce wa sarki, “Bawanka zai aikata dukan abin da ranka yă daɗe sarki, ya umarce shi.” Saboda haka Mefiboshet ya riƙa ci a teburin Dawuda kamar sauran’ya’yan sarki.
12 Now Mephibosheth had a young son whose name was Mica. Truly, all the kindred of the house of Ziba served Mephibosheth.
Mefiboshet yana da wani ƙaramin ɗa sunansa Mika, dukan iyalin gidan Ziba kuwa bayin Mefiboshet ne.
13 But Mephibosheth lived in Jerusalem. For he was fed always from the table of the king. And he was lame in both feet.
Mefiboshet ya zauna a Urushalima, gama kullum yana ci a teburin sarki, shi kuwa gurgu ne a dukan ƙafafu.

< 2 Samuel 9 >