< 2 Samuel 7 >

1 Now it happened that, when the king had settled in his house, and the Lord had given him rest on every side from all his enemies,
Bayan sarki ya kama zama a fadansa Ubangiji kuma ya hutashe shi daga dukan abokan gābansa da suke kewaye da shi,
2 he said to the prophet Nathan, “Do you not see that I live in a house of cedar, and that the ark of God has been placed in the midst of tent skins?”
sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar katakon al’ul, amma akwatin alkawarin Allah yana zaune a tenti.”
3 And Nathan said to the king: “Go, do all that is in your heart. For the Lord is with you.”
Natan ya amsa wa sarki ya ce, “Duk abin da yake a zuciyarka, sai ka yi, gama Ubangiji yana tare da kai.”
4 But it happened in that night, behold, the word of the Lord came to Nathan, saying:
A daren nan maganar Ubangiji ta zo wa Natan cewa,
5 “Go, and say to my servant David: ‘Thus says the Lord: Should you build a house for me as a dwelling place?
“Je ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, kai ne za ka gina mini gida in zauna?
6 For I have not lived in a house from the day that I led the sons of Israel away from the land of Egypt, even to this day. Instead, I have walked in a tabernacle, and in a tent.
Ban taɓa zama a gida ba tun daga ranar da na fito da Isra’ilawa daga Masar har yă zuwa yau. Ina dai kai da kawowa a tenti, a matsayin mazaunina.
7 And in all the places that I have crossed through, with all the sons of Israel, did I ever speak a word to anyone from the tribes of Israel, whom I instructed to pasture my people Israel, saying: Why have you not built me a house of cedar?’
A cikin kaiwa da kawowar da nake yi cikin dukan Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani shugabanninsu wanda na umarta su lura da mutanena Isra’ila, “Don me ba ku gina mini mazauni da katakon al’ul ba?”’
8 And now, so shall you speak to my servant David: ‘Thus says the Lord of hosts: I took you from the pastures, from following the sheep, so that you would be the leader over my people Israel.
“Yanzu, ka gaya wa bawana Dawuda ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauko ka daga makiyaya, daga kuma garken tumaki ka zama sarki bisan mutane Isra’ila.
9 And I have been with you everywhere that you walked. And I have slain all your enemies before your face. And I have made you a great name, beside the name of the great ones who are upon the earth.
Na kasance tare da kai duk inda ka tafi, na kuma kawar da dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka yă shahara kamar sunayen shahararrun mutanen duniya.
10 And I will appoint a place for my people Israel, and I will plant them, and they shall live there, and they shall no longer be disturbed. Neither shall the sons of iniquity continue to afflict them as before,
Zan kuma tanada wa mutanena Isra’ila wuri, in kuma dasa su yadda za su kasance da gida kansu ba tare da an ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara wahalshe su kamar dā ba,
11 from the day when I appointed judges over my people Israel. And I will give rest to you from all your enemies. And the Lord foretells to you that the Lord himself will make a house for you.
yadda suka yi tun lokacin da na naɗa shugabanni bisan mutanena Isra’ila, zan kuma hutashe ka daga hannun abokan gābanka. “‘Ubangiji ya furta maka cewa Ubangiji kansa zai kafa maka gida.
12 And when your days will have been fulfilled, and you will sleep with your fathers, I will raise up your offspring after you, who will go forth from your loins, and I will make firm his kingdom.
Sa’ad da kwanakinka suka ƙare, za ka huta tare da kakanninka, zan tā da zuriyarka, na cikinka, zan kuma sa mulkinsa ya kahu.
13 He himself shall build a house to my name. And I will establish the throne of his kingdom, even forever.
Shi zai gina gida domin Sunana, zan kuwa kafa gadon sarautarsa har abada.
14 I will be a father to him, and he shall be a son to me. And if he will commit any iniquity, I will correct him with the rod of men and with the wounds of the sons of men.
Zan zama Ubansa, shi kuma yă zama ɗana. Idan ya yi laifi, zan yi amfani da mutane in hukunta shi. Mutane ne za su zama bulalata.
15 But my mercy I will not take away from him, as I took it away from Saul, whom I removed from before my face.
Amma ba za a taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi yadda na ɗauke ta daga wurin Shawulu ba, shi wannan wanda na kawar daga gabanka.
16 And your house shall be faithful, and your kingdom shall be before your face, for eternity, and your throne shall be secure continuously.’”
Gidanka da kuma masarautarka za su dawwama har abada a gabana; gadon sarautarka kuma zai kahu har abada.’”
17 According to all these words, and according to this entire vision, so did Nathan speak to David.
Natan ya gaya wa Dawuda dukan abin da Allah ya bayyana masa.
18 Then king David entered and sat before the Lord, and he said: “Who am I, O Lord God, and what is my house, that you would bring me to this point?
Sa’an nan Sarki Dawuda ya je ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ko gidana, har da ka ɗaga mu zuwa wannan matsayi?
19 Moreover, this has seemed little in your sight, O Lord God, unless you also will speak about the house of your servant for a long time. For this is the law of Adam, O Lord God.
Har ya zama kamar wannan bai isa ba a gabanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka kuma yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Haka ka saba yi da mutane, ya Ubangiji Mai Iko Duka?
20 Therefore, what more will David be able to say to you? For you know your servant, O Lord God.
“Me kuma Dawuda zai ce maka? Gama ka san bawanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka.
21 Because of your word, and according to your own heart, you have done all these great deeds, so that you would make it known to your servant.
Gama saboda maganarka da kuma bisa ga nufinka, ka aikata wannan babban abu, ka kuma sanar da bawanka.
22 For this reason, you are magnified, O Lord God. For there is no one like you. And there is no God except you, in all the things that we have heard with our own ears.
“Kai mai girma ne, ya Ubangiji Mai Iko Duka! Babu wani kamar ka, babu kuma wani Allah sai kai; kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
23 But what nation is there upon the earth like your people Israel, because of whom God went forth, so that he might redeem a people for himself, and establish a name for himself, and accomplish for them great and terrible things upon the earth, before the face of your people, whom you redeemed for yourself away from Egypt, the nations and their gods.
Wane ne kuma yake kamar da mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allah ya fita don yă kuɓutar wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa da kuma al’amuran banmamaki ta wurin korin al’ummai da allolinsu daga gaban mutanenka, waɗanda ka kuɓutar daga Masar?
24 For you have secured your people Israel for yourself, as an everlasting people. And you, O Lord God, have become their God.
Ka kafa mutanenka Isra’ila kamar naka na kanka har abada, kai kuma, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
25 Now therefore, O Lord God, raise up forever the word that you have spoken over your servant and over his house. And do just as you have said,
“Yanzu kuwa, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa. Ka yi kamar yadda ka alkawarta,
26 so that your name may be magnified even forever, and so that it may be said: ‘The Lord of hosts is the God over Israel.’ And the house of your servant David will be established in the sight of the Lord.
domin sunanka yă kasance da girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah ne a bisa Isra’ila!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
27 For you, O Lord of hosts, God of Israel, have revealed to the ear of your servant, saying, ‘I will build a house for you.’ Because of this, your servant has found it in his heart to pray this prayer to you.
“Ya Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka bayyana wa bawanka cewa, ‘Zan gina maka gida.’ Saboda haka bawanka ya sami ƙarfin hali yă miƙa maka wannan addu’a.
28 Now therefore, O Lord God, you are God, and your words shall be true. For you have spoken to your servant these good things.
Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai Allah ne! Maganarka da aminci take, ka kuma yi wa bawanka waɗannan abubuwa masu kyau.
29 Therefore, begin, and bless the house of your servant, so that it may be forever before you. For you, O Lord God, have spoken. And so, let the house of your servant be blessed with your blessing forever.”
In ya gamshe ka, bari ka albarkaci gidan bawanka don yă dawwama a gabanka har abada; gama kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka riga ka yi magana, kuma saboda kai ka sa albarka ga gidan bawanka, lalle zai kasance da albarka har abada.”

< 2 Samuel 7 >