< 2 Samuel 21 >

1 And a famine occurred, during the days of David, for three years continuously. And David consulted the oracle of the Lord. And the Lord said: “This is because of Saul, and his house of bloodshed. For he killed the Gibeonites.”
Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
2 Therefore, the king, calling for the Gibeonites, spoke to them. Now the Gibeonites were not of the sons of Israel, but were the remnant of the Amorites. And the sons of Israel had sworn an oath to them, but Saul wished to strike them in zeal, as if on behalf of the sons of Israel and Judah.
Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
3 Therefore, David said to the Gibeonites: “What shall I do for you? And what shall be your satisfaction, so that you may bless the inheritance of the Lord?”
Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
4 And the Gibeonites said to him: “There is no quarrel for us over silver or gold, but against Saul and against his house. And we do not desire that any man of Israel be put to death.” The king said to them, “Then what do you wish that I should do for you?”
Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
5 And they said to the king: “The man who unjustly afflicted and oppressed us, we ought to destroy in such manner that not even one of his stock may be left behind in all the parts of Israel.
Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
6 Let seven men from his sons be given to us, so that we may crucify them to the Lord in Gibeon of Saul, formerly the chosen place of the Lord.” And the king said, “I will give them.”
a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
7 But the king spared Mephibosheth, the son of Jonathan, the son of Saul, because of the oath of the Lord which had been made between David and Jonathan, the son of Saul.
Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
8 And so the king took the two sons of Rizpah, the daughter of Aiah, whom she bore to Saul, Armoni and Mephibosheth, and the five sons of Michal, the daughter of Saul, whom she conceived of Adriel, the son of Barzillai, who was from Meholath,
Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
9 and he gave them into the hands of the Gibeonites. And they crucified them on a hill in the sight of the Lord. And these seven fell together in the first days of the harvest, when the barley is beginning to be reaped.
Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
10 Then Rizpah, the daughter of Aiah, taking a haircloth, spread it under herself on a rock, from the beginning of the harvest until water dropped from heaven upon them. And she did not permit the birds to tear them by day, nor the beasts by night.
Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
11 And it was reported to David what Rizpah, the daughter of Aiah, the concubine of Saul, had done.
Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
12 And David went and took the bones of Saul, and the bones of his son Jonathan, from the men of Jabesh Gilead, who had stolen them from the street of Bethshan, where the Philistines had suspended them after they had slain Saul at Gilboa.
sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
13 And he brought the bones of Saul, and the bones of his son Jonathan, from there. And they collected the bones of those who had been crucified.
Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
14 And they buried them with the bones of Saul and his son Jonathan, in the land of Benjamin, to the side of the sepulcher of his father Kish. And they did all that the king had instructed. And after these things, God showed favor again to the land.
Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
15 Then the Philistines again undertook a battle against Israel. And David descended, and his servants with him, and they fought against the Philistines. But when David grew faint,
Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
16 Ishbibenob, who was of the ancestry of Arapha, the iron of whose spear weighed three hundred ounces, who had been girded with a new sword, strove to strike down David.
Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
17 And Abishai, the son of Zeruiah, defended him, and striking the Philistine, he killed him. Then David’s men swore an oath to him, saying, “You shall no longer go out to war with us, lest you extinguish the lamp of Israel.”
Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
18 Also, a second war occurred in Gob against the Philistines. Then Sibbecai from Hushah struck down Saph, from the stock of Arapha, of the ancestry of the giants.
Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
19 Then there was a third war in Gob against the Philistines, in which Adeodatus, a son of the forest, a weaver from Bethlehem, struck down Goliath the Gittite, the shaft of whose spear was like the beam used by a cloth maker.
Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
20 A fourth battle was in Gath. In that place, there was a lofty man, who had six digits on each hand and each foot, that is, twenty-four in all, and he was from the origins of Arapha.
Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
21 And he blasphemed Israel. So Jonathan, the son of Shimei, the brother of David, struck him down.
Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
22 These four men were born of Arapha in Gath, and they fell by the hand of David and his servants.
Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.

< 2 Samuel 21 >