< 2 Samuel 20 >

1 And it happened that there was, in that place, a man of Belial, whose name was Sheba, the son of Bichri, a man of Benjamin. And he sounded the trumpet, and he said: “There is no portion for us in David, nor any inheritance in the son of Jesse. Return to your own tents, O Israel.”
Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
2 And all of Israel separated from David, and they were following Sheba, the son of Bichri. But the men of Judah clung to their king, from the Jordan as far as Jerusalem.
Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
3 And when the king had entered his house at Jerusalem, he took the ten women concubines, whom he had left behind to care for the house, and he put them into custody, allowing them provisions. But he did not enter to them. Instead, they were enclosed, even until the day of their deaths, living as widows.
Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
4 Then the king said to Amasa, “Summon to me all the men of Judah on the third day, and you shall be present also.”
Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
5 Therefore, Amasa went away, so that he might summon Judah. But he delayed beyond the agreed time that the king had appointed to him.
Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
6 And David said to Abishai: “Now Sheba, the son of Bichri, will afflict us more so than Absalom did. Therefore, take the servants of your lord, and pursue him, otherwise he may find fortified cities, and escape from us.”
Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
7 And so, the men of Joab departed with him, along with the Cherethites and the Pelethites. And all the able-bodied men went out from Jerusalem to pursue Sheba, the son of Bichri.
Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
8 And when they were beside the great stone, which is in Gibeon, Amasa came to meet them. Now Joab was wearing a close-fitting coat of equal length with his garment. And over these, he was girded with a sword hanging down to his thigh, in a scabbard which was made so that the sword could be removed with the least motion, and then strike.
Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
9 Then Joab said to Amasa, “Be well, my brother.” And he held Amasa by the chin with his right hand, as if to kiss him.
Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
10 But Amasa did not notice the sword that Joab had. And he struck him in the side, and his intestines poured out to the ground. And he did not inflict a second wound, and he died. Then Joab and his brother Abishai pursued Sheba, the son of Bichri.
Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
11 Meanwhile, certain men, from the company of Joab, when they had stopped beside the dead body of Amasa, said: “Behold, the one who wished to be in the place of Joab, the companion of David.”
Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
12 Now Amasa was covered with blood, and was lying in the middle of the road. A certain man saw this, with all the people standing nearby to look at him, and he removed Amasa from the road into a field. And he covered him with a garment, so that those passing by would not stop because of him.
Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
13 Then, when he had been removed from the road, all the men continued on, following Joab in the pursuit of Sheba, the son of Bichri.
Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
14 Now he had passed through all the tribes of Israel into Abel and Bethmaacah. And all the elect men had gathered together to him.
Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
15 And so, they went and besieged him at Abel and Bethmaacah. And they surrounded the city with siege works, and the city was blockaded. Then the entire crowd who were with Joab strove to destroy the walls.
Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
16 And a wise woman exclaimed from the city: “Listen, listen, and say to Joab: Draw near, and I will speak with you.”
Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
17 And when he had drawn near to her, she said to him, “Are you Joab?” And he responded, “I am.” And she spoke in this way to him, “Listen to the words of your handmaid.” He responded, “I am listening.”
Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
18 And again she spoke: “A word was said in the old proverb, ‘Those who would inquire, let them inquire in Abel.’ And so they would reach a conclusion.
Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
19 Am I not the one who responds with the truth in Israel? And yet you are seeking to overthrow the city, and to overturn a mother in Israel! Why would you cast down the inheritance of the Lord?”
Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
20 And responding, Joab said: “May this be far, may this be far from me! May I not cast down, and may I not demolish.
Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
21 The matter is not as you said. Rather, a man from mount Ephraim, Sheba, the son of Bichri, by name, has lifted up his hand against king David. Deliver him alone, and we will withdraw from the city.” And the woman said to Joab, “Behold, his head will be thrown down to you from the wall.’
Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
22 Therefore, she entered to all the people, and she spoke to them wisely. And they cut off the head of Sheba, the son of Bichri, and they threw it down to Joab. And he sounded the trumpet, and they withdrew from the city, each one to his own tent. But Joab returned to Jerusalem to the king.
Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
23 Thus Joab was over the entire army of Israel. And Benaiah, the son of Jehoiada, was over the Cerethites and Phelethites.
Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
24 Yet truly, Adoram was over the tributes. And Jehoshaphat, the son of Ahilud, was the keeper of records.
Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
25 Now Sheva was the scribe. And truly Zadok and Abiathar were the priests.
Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
26 But Ira, the Jairite, was the priest of David.
Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.

< 2 Samuel 20 >